< Salme 2 >

1 Hvorfor fnyser Hedninger, hvi pønser Folkefærd paa, hvad faafængt er?
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 Jordens Konger rejser sig, Fyrster samles til Raad mod HERREN og mod hans Salvede:
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 »Lad os sprænge deres Baand og kaste Rebene af os!«
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 Han, som troner i Himlen, ler, Herren, han spotter dem.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Saa taler han til dem i Vrede, forfærder dem i sin Harme:
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 »Jeg har dog indsat min Konge paa Zion, mit hellige Bjerg!«
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 Jeg kundgør HERRENS Tilsagn. Han sagde til mig: »Du er min Søn, jeg har født dig i Dag!
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Bed mig, og jeg giver dig Hedningefolk til Arv og den vide Jord i Eje;
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 med Jernspir skal du knuse dem og sønderslaa dem som en Pottemagers Kar!«
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 Og nu, I Konger, vær kloge, lad eder raade, I Jordens Dommere,
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 tjener HERREN i Frygt, fryd jer med Bæven!
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Kysser Sønnen, at ikke han vredes og I forgaar! Snart blusser hans Vrede op. Salig hver den, der lider paa ham!
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Salme 2 >