< Salme 139 >
1 Til Sangmesteren. Af David. En Salme. HERRE, du ransager mig og kender mig!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 Du ved, naar jeg sidder, og naar jeg staar op, du fatter min Tanke i Frastand,
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 du har Rede paa, hvor jeg gaar eller ligger, og alle mine Veje kender du grant.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Thi før Ordet er til paa min Tunge, se, da ved du det, HERRE, til fulde.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Bagfra og forfra omslutter du mig, du lægger din Haand paa mig.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 At fatte det er mig for underfuldt, for højt, jeg evner det ikke!
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Hvorhen skal jeg gaa for din Aand, og hvor skal jeg fly for dit Aasyn?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 Farer jeg op til Himlen, da er du der, reder jeg Leje i Dødsriget, saa er du der; (Sheol )
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
9 tager jeg Morgenrødens Vinger, fæster jeg Bo, hvor Havet ender,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 da vil din Haand ogsaa lede mig der, din højre holde mig fast!
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 Og siger jeg: »Mørket skal skjule mig, Lyset blive Nat omkring mig!«
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 saa er Mørket ej mørkt for dig, og Natten er klar som Dagen, Mørket er som Lyset.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 Thi du har dannet mine Nyrer, vævet mig i Moders Liv.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 Jeg vil takke dig, fordi jeg er underfuldt skabt; underfulde er dine Gerninger, det kender min Sjæl til fulde.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 Mine Ben var ikke skjult for dig, da jeg blev skabt i Løndom, virket i Jordens Dyb;
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 som Foster saa dine Øjne mig, i din Bog var de alle skrevet, Dagene var bestemt, før en eneste af dem var kommet.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 Hvor kostelige er dine Tanker mig, Gud, hvor stor er dog deres Sum!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 Tæller jeg dem, er de flere end Sandet, jeg vaagner — og end er jeg hos dig.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 Vilde du dog dræbe de gudløse, Gud, maatte Blodets Mænd vige fra mig,
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 de, som taler om dig paa Skrømt og sværger falsk ved dit Navn.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Jeg hader jo dem, der hader dig, HERRE, og væmmes ved dem, der staar dig imod;
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 med fuldt Had hader jeg dem, de er ogsaa mine Fjender.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Ransag mig, Gud, og kend mit Hjerte, prøv mig og kend mine Tanker!
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 Se, om jeg er paa Smertens Vej, og led mig paa Evigheds Vej!
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.