< Ordsprogene 1 >

1 Ordsprog af Salomo, Davids Søn, Israels Konge.
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 Af dem skal man lære Visdom forstandig Tale,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 tage mod Tugt, som gør klog, mod Retfærdighed, Ret og Retsind;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 de skal give tankeløse Klogskab, ungdommen Kundskab og Kløgt;
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 den vise høre og øge sin Viden, den forstandige vinde sig Levekunst;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 de skal lære at tyde Ordsprog og Billeder, de vises Ord og Gaader.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 HERRENS Frygt er Kundskabs begyndelse, Daarer ringeagter Visdom og Tugt.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Hør, min Søn, paa din Faders Tugt, opgiv ikke din Moders Belæring.
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 thi begge er en yndig Krans til dit Hoved og Kæder til din Hals.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Min Søn, sig nej, naar Syndere lokker!
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Siger de: »Kom med, lad os lure paa den fromme, lægge Baghold for sagesløs, skyldfri Mand!
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Som Dødsriget sluger vi dem levende, med Hud og Haar, som for de i Graven. (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 Vi vinder os Gods og Guld, vi fylder vore Huse med Rov.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Gør fælles Sag med os; vi har alle fælles Pung!«
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 — min Søn, gaa da ikke med dem, hold din Fod fra deres Sti;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 thi deres Fødder løber efter ondt, de haster for at udgyde Blod.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Thi det er unyttigt at udspænde Garnet for alle Fugles Øjne;
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 de lurer paa eget Blod, lægger Baghold for eget Liv.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Saa gaar det enhver, der attraar Rov, det tager sin Herres Liv.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Visdommen raaber paa Gaden, paa Torvene løfter den Røsten;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 oppe paa Murene kalder den, tager til Orde i Byen ved Portindgangene:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Hvor længe vil I tankeløse elske Tankeløshed, Spotterne finde deres Glæde i Spot og Daarerne hade Kundskab?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Vend eder til min Revselse! Se, jeg lader min Aand udvælde for eder, jeg kundgør eder mine Ord:
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Fordi jeg raabte og I stod imod, jeg vinked og ingen ænsed det,
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 men I lod haant om alt mit Raad og tog ikke min Revselse til jer,
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 derfor ler jeg ved eders Ulykke, spotter, naar det, I frygter, kommer,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 naar det, I frygter, kommer som Uvejr, naar eders Ulykke kommer som Storm, naar Trængsel og Nød kommer over jer.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Da svarer jeg ej, naar de kalder, de søger mig uden at finde,
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 fordi de hadede Kundskab og ikke valgte HERRENS Frygt;
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 mit Raad tog de ikke til sig, men lod haant om al min Revselse.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Frugt af deres Færd skal de nyde og mættes med egne Raad;
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 thi tankeløses Egensind bliver deres Død, Taabers Sorgløshed bliver deres Undergang;
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 men den, der adlyder mig, bor trygt, sikret mod Ulykkens Rædsel.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Ordsprogene 1 >