< 4 Mosebog 25 >
1 Israeliterne slog sig derpaa ned i Sjittim. Men Folket begyndte at bedrive Hor med de moabitiske Kvinder;
Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
2 og da de indbød Folket til deres Guders Slagtofre, spiste Folket deraf og tilbad deres Guder.
waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
3 Og Israel holdt til med Ba'al-Peor; derover blussede HERRENS Vrede op mod Israel,
Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
4 og HERREN sagde til Moses: »Kald alle Folkets Overhoveder sammen og hæng dem op for HERREN under aaben Himmel, for at HERRENS Vrede maa vige fra Israel!«
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
5 Og Moses sagde til Israeliternes Dommere: »Enhver af eder skal slaa dem af sine Mænd ihjel, der har holdt til med Ba'al-Peor!«
Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
6 Og se, en af Israeliterne kom og førte en midjanitisk Kvinde hen til sine Landsmænd lige for Øjnene af Moses og hele Israeliternes Menighed, medens de stod og græd ved Indgangen til Aabenbaringsteltet.
Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
7 Da nu Pinehas, Præsten Arons Søn Eleazars Søn, saa det, traadte han frem af Menighedens Midte, greb et Spyd,
Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
8 fulgte den israelitiske Mand ind i Sengekammeret og gennemborede dem begge, baade den israelitiske Mand og Kvinden, hende gennem Underlivet. Da standsede Plagen blandt Israeliterne.
ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
9 Men Tallet paa dem, Plagen havde kostet Livet, løb op til 24 000.
Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
10 Da talede HERREN saaledes til Moses:
Ubangiji ya ce wa Musa,
11 »Pinehas, Præsten Arons Søn Eleazars Søn, har vendt min Vrede fra Israeliterne, idet han var nidkær iblandt dem med min Nidkærhed, saa at jeg ikke tilintetgjorde Israeliterne i min Nidkærhed.
“Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
12 Derfor skal du sige: Se, jeg giver ham min Fredspagt!
Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
13 Et evigt Præstedømmes Pagt skal blive hans og efter ham hans Efterkommeres Lod, til Løn for at han var nidkær for sin Gud og skaffede Israeliterne Soning.«
Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
14 Den dræbte Israelit, han, der dræbtes sammen med den midjanitiske Kvinde, hed Zimri, Salus Søn, og var Øverste for et Fædrenehus blandt Simeoniterne;
Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
15 og den dræbte midjanitiske Kvinde hed Kozbi og var en Datter af Zur, der var Stammehøvding for et Fædrenehus blandt Midjaniterne,
Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
16 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 »Fald over Midjaniterne og slaa dem;
“Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
18 thi de faldt over eder med de Rænker, de spandt imod eder i den Sag med Peor og med Kozbi, den midjanitiske Høvdings Datter, deres Landsmandinde, der dræbtes, den Dag Plagen brød løs for Peors Skyld.«
gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”