< 4 Mosebog 21 >
1 Men da Kana'anæeren, Kongen af Arad, der boede i Sydlandet, hørte, at Israel rykkede frem ad Atarimvejen, angreb han Israel og tog nogle af dem til Fange.
Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
2 Da aflagde Israel et Løfte til HERREN og sagde: »Hvis du giver dette Folk i min Haand, vil jeg lægge Band paa deres Byer!«
Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
3 Og HERREN hørte Israels Røst og gav Kana'anæerne i deres Haand, hvorefter de lagde Band paa dem og deres Byer. Derfor gav man Stedet Navnet Horma.
Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
4 Saa brød de op fra Bjerget Hor i Retning af det røde Hav for at komme uden om Edoms Land. Undervejs blev Folket utaalmodigt
Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
5 og talte mod Gud og Moses og sagde: »Hvorfor førte I os ud af Ægypten, naar vi skal dø i Ørkenen? Her er jo hverken Brød eller Vand, og vi er lede ved denne usle Føde.«
suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
6 Da sendte HERREN Giftslanger blandt Folket, og de bed Folket saa en Mængde af Israel døde.
Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
7 Saa kom Folket til Moses og sagde: »Vi har syndet ved at tale imod HERREN og dig; gaa i Forbøn hos HERREN, at han tager Slangerne fra os!« Og Moses gik i Forbøn for Folket.
Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
8 Da sagde HERREN til Moses: »Lav dig en Slange og sæt den paa en Stang, saa skal enhver slangebidt, der ser hen paa den, leve!«
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
9 Da lavede Moses en Kobberslange og satte den paa en Stang; og enhver, der saa hen paa Kobberslangen, naar en Slange havde bidt ham, beholdt Livet.
Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
10 Saa brød Israeliterne op og slog Lejr i Obot;
Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
11 og de brød op fra Obot og slog Lejr i Ijje-Ha'abarim i Ørkenen østen for Moab.
Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
12 Derfra brød de op og slog Lejr i Zereddalen.
Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
13 Derfra brød de op og slog Lejr i Ørkenen hinsides Arnon, som udspringer paa Amoriternes Omraade, thi Arnon var Moabs Grænse mod Amoriterne.
Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14 Derfor hedder det i Bogen om HERRENS Krige: .... Vaheb i Sufa og Dalene, Arnon og Dalenes Skrænt,
Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
15 som strækker sig til Ars Sæde og læner sig til Moabs Grænse.
da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
16 Derfra brød de op til Be'er; det er det Be'er, HERREN havde for Øje, da han sagde til Moses: »Kald Folket sammen, saa vil jeg give dem Vand!«
Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
17 Da sang Israeliterne denne Sang: Brønd, væld frem! Syng til dens Pris!
Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
18 Brønd, som Høvdinger grov, som Folkets ædle bored med Herskerspir og Stave! Fra Ørkenen brød de op til Mattana;
game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
19 fra Mattana til Nahaliel; fra Nahaliel til Bamot;
daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
20 fra Bamot til Dalen paa Moabs Højslette, til Pisgas Top, som rager op over Ørkenen.
daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
21 Israel sendte nu Sendebud til Amoriterkongen Sihon og lod sige:
Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
22 »Lad mig faa Lov at drage igennem dit Land! Vi vil ikke dreje ind paa Marker eller i Vinhaver, vi vil ikke drikke Vand af Brøndene, vi vil følge Kongevejen, indtil vi er naaet igennem dit Land!«
“Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
23 Men Sihon tillod ikke Israel at drage igennem sit Land; derimod samlede han alt sit Krigsfolk og rykkede ud i Ørkenen imod Israel, og da han naaede Jaza, angreb han Israel.
Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
24 Men Israel slog ham med Sværdet og underlagde sig hans Land fra Arnon til Jabbok, til Ammoniternes Land; thi Ja'zer ligger ved Ammoniternes Grænse;
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
25 og Israel indtog alle disse Byer, og Israel bosatte sig i alle Amoriternes Byer, i Hesjbon og alle tilhørende Smaabyer.
Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
26 Thi Hesjbon var Amoriterkongen Sihons By; han havde angrebet Moabs forrige Konge og frataget ham hele hans Land indtil Arnon.
Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
27 Derfor synger Skjaldene: Kom hid til Hesjbon, lad den blive bygget og grundfæstet, Sihons By!
Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
28 Thi Ild for ud fra Hesjbon, Ildslue fra Sihons Stad, den fortærede Moabs Byer, opaad Arnons Højder.
“Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
29 Ve dig, Moab! Det er ude med dig, Kemosj's Folk! Han gjorde sine Sønner til Flygtninge og sine Døtre til Krigsfanger for Sihon, Amoriternes Konge.
Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
30 Og vi skød dem ned, Hesjbon er tabt indtil Dibon; vi lagde dem øde til Nofa, som ligger ved Medeba.
“Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
31 Saa bosatte Israel sig i Amoriternes Land.
Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
32 Derpaa sendte Moses Spejdere til Ja'zer; og de erobrede det tillige med tilhørende Smaabyer, og han drev de der boende Amoriter bort.
Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
33 Derpaa vendte de om og drog ad Basan til. Da rykkede Og, Kongen af Basan, ud imod dem med alle sine Krigere og angreb dem ved Edre'i.
Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
34 Men HERREN sagde til Moses: »Frygt ikke for ham! Thi jeg giver ham og alle hans Krigere og hans Land i din Haand, saa at du kan handle med ham, som du handlede med Amoriterkongen Sihon, der boede i Hesjbon.«
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
35 Da slog de ham og hans Sønner og alle hans Krigere, saa at ikke en eneste af dem undslap, og derpaa underlagde de sig hans Land.
Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.