< 4 Mosebog 18 >
1 HERREN sagde til Aron: Du tillige med dine Sønner og dit Fædrenehus skal have Ansvaret for Helligdommen, og du tillige med dine Sønner skal have Ansvaret for eders Præstetjeneste.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
2 Men ogsaa dine Brødre, Levis Stamme, din Fædrenestamme, skal du lade træde frem sammen med dig, og de skal holde sig til dig og gaa dig til Haande, naar du tillige med dine Sønner gør Tjeneste foran Vidnesbyrdets Telt;
Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
3 og de skal tage Vare paa, hvad du har at varetage, og paa alt, hvad der er at varetage ved Teltet, men de maa ikke komme de hellige Ting eller Alteret nær, at ikke baade de og I skal dø.
Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
4 De skal holde sig til dig og tage Vare paa, hvad der er at varetage ved Aabenbaringsteltet, alt Arbejdet derved, men ingen Lægmand maa der komme eder nær.
Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
5 Men I skal tage Vare paa, hvad der er at varetage ved Helligdommen og Alteret, for at der ikke atter skal komme Vrede over Israeliterne.
“Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
6 Se, jeg har selv udtaget eders Brødre Leviterne af Israeliternes Midte som en Gave til eder, de er givet HERREN til at udføre Arbejdet ved Aabenbaringsteltet.
Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
7 Men du tillige med dine Sønner skal tage Vare paa eders Præstegerning i alt, hvad der angaar Alteret og det, der er inden for Forhænget, og udføre Arbejdet derved. Som en Gave skænker jeg eder Præstedømmet; men enhver Lægmand, der trænger sig ind deri, skal lide Døden.
Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
8 HERREN talede fremdeles til Aron: Se, jeg giver dig, hvad der skal lægges til Side af mine Offerydelser; alle Israeliternes Helliggaver giver jeg dig og dine Sønner som eders Del, en evig gyldig Rettighed.
Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
9 Følgende skal tilfalde dig af det højhellige, fraregnet hvad der opbrændes: Alle deres Offergaver, der falder ind under Afgrødeofre, Syndofre og Skyldofre, som de bringer mig til Erstatning; som højhelligt skal dette tilfalde dig og dine Sønner.
Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
10 Paa et højhelligt Sted skal du spise det, og alle af Mandkøn maa spise deraf; det skal være dig helligt.
Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
11 Fremdeles skal følgende tilfalde dig som Offerydelse af deres Gaver: Alle Gaver fra Israeliterne, hvormed der udføres Svingning, giver jeg dig tillige med dine Sønner og Døtre som en evig gyldig Rettighed; enhver, som er ren i dit Hus, maa spise deraf.
“Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
12 Alt det bedste af Olien, Mosten og Kornet, Førstegrøden deraf, som de giver HERREN, giver jeg dig.
“Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
13 De første Frugter af alt, hvad der gror i deres Land, som de bringer HERREN, skal tilfalde dig; enhver, som er ren i dit Hus, maa spise deraf.
Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
14 Alt, hvad der lægges Band paa i Israel, skal tilfalde dig.
“Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
15 Af alt Kød, som de bringer til HERREN, saavel af Mennesker som af Dyr, skal alt, hvad der aabner Moders Liv, tilfalde dig; dog skal du lade de førstefødte Mennesker udløse, og ligeledes skal du lade de førstefødte urene Dyr udløse.
Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
16 Hine skal du lade udløse, naar de er en Maaned gamle eller derover, med en Vurderingssum af fem Sekel efter hellig Vægt, tyve Gera paa en Sekel.
Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
17 Men de førstefødte Stykker Hornkvæg, Lam eller Geder maa du ikke lade udløse; de er hellige, deres Blod skal du sprænge paa Alteret, og Fedtet skal du bringe som Røgoffer, et Ildoffer til en liflig Duft for HERREN;
“Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
18 men Kødet tilfalder dig; ligesom Svingningsbrystet og højre Kølle tilfalder det dig.
Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
19 Al Offerydelse af Helliggaver, som Israeliterne yder HERREN, giver jeg dig tillige med dine Sønner og Døtre som en evig gyldig Rettighed; det skal være en evig gyldig Saltpagt for HERRENS Aasyn for dig tillige med dine Efterkommere.
Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
20 HERREN sagde fremdeles til Aron: Du skal ingen Arvelod have i deres Land, og der skal ikke tilfalde dig nogen Lod iblandt dem; jeg selv er din Arvelod og Del blandt Israeliterne.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
21 Men se, Levisønnerne giver jeg al Tiende i Israel som Arvelod til Løn for det Arbejde, de udfører ved Aabenbaringsteltet.
“Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
22 Israeliterne maa herefter ikke komme Aabenbaringsteltet nær, for at de ikke skal paadrage sig Synd og dø;
Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
23 kun Leviterne maa udføre Arbejdet ved Aabenbaringsteltet, og de skal have Ansvaret derfor. Det skal være eder en evig gyldig Anordning fra Slægt til Slægt. Men nogen Arvelod skal de ikke have blandt Israeliterne;
Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
24 thi Tienden, Israeliterne yder HERREN som Offerydelse, giver jeg Leviterne til Arvelod. Derfor sagde jeg dem, at de ikke skal have nogen Arvelod blandt Israeliterne.
A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
25 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
26 Tal til Leviterne og sig til dem: Naar I af Israeliterne modtager Tienden, som jeg har givet eder som den Arvelod, I skal have af dem, saa skal I yde HERREN en Offerydelse deraf, Tiende af Tienden;
“Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
27 og denne eders Offerydelse skal ligestilles med Offerydelsen af Kornet fra Tærskepladsen og Overfloden fra Vinpersen.
Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
28 Saaledes skal ogsaa I yde HERREN en Offerydelse af al den Tiende, I modtager af Israeliterne, og denne HERRENS Offerydelse skal I give Præsten Aron.
Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
29 Af alle de Gaver, I modtager, skal I yde HERRENS Offerydelse, af alt det bedste deraf, som hans Helliggave.
Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
30 Og sig til dem: Naar I yder det bedste deraf, skal det ligestilles med Offerydelsen af, hvad der kommer fra Tærskepladsen og Vinpersen.
“Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
31 I maa spise det hvor som helst sammen med eders Familie, thi det er eders Løn for eders Arbejde ved Aabenbaringsteltet.
Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
32 Naar I blot yder det bedste deraf, skal I ikke for den Sags Skyld paadrage eder Synd og ikke vanhellige Israeliternes Helliggaver og udsætte eder for at dø.
Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”