< Nehemias 12 >
1 Følgende er Præsterne og Leviter, der drog op med Zerubbabel, Sjealtiels Søn, og Jesua: Seraja, Jirmeja, Ezra,
Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
2 Amarja, Malluk, Hattusj.
Amariya, Malluk, Hattush
3 Sjekanja, Harim, Meremot,
Shekaniya, Rehum, Meremot,
5 Mijjamin, Ma'adja, Bilga,
Miyamin, Mowadiya, Bilga,
6 Sjemaja, Jojarib, Jedaja,
Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
7 Sallu, Amok, Hilkija og Jedaja. Det var Overhovederne for Præsterne og deres Brødre paa Jesuas Tid.
Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
8 Leviterne: Jesua, Binnuj, Kadmiel, Sjerebja, Juda, Mattanja, der sammen med sine Brødre forestod Lovsangen,
Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
9 medens Bakbukja og Unni sammen med deres Brødre stod over for dem efter deres Afdelinger.
Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
10 Jesua avlede Jojakim, Jojakim avlede Eljasjib, Eljasjib avlede Jojada,
Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
11 Jojada avlede Johanan, og Johanan avlede Jaddua.
Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
12 Paa Jojakims Tid var Overhovederne for Præsternes Fædrenehuse følgende: Meraja for Seraja, Hananja for Jirmeja,
A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
13 Mesjullam for Ezra, Johanan for Amarja,
na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
14 Jonatan for Malluk, Josef for Sjebanja,
na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
15 Adna for Harim, Helkaj for Merajot,
na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
16 Zekarja for Iddo, Mesjullam for Ginneton,
na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
17 Zikri for Abija, .... for Minjamin, Piltaj for Ma'adja,
na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
18 Sjammua for Bilga, Jonatan for Sjemaja,
na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
19 Mattenaj for Jojarib, Uzzi for Jedaja,
na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
20 Kallaj for Sallu, Eber for Amok,
na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
21 Hasjabja for Hilkija og Netan'el for Jedaja.
na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
22 Leviterne: .... . I Eljasjibs, Jojadas, Johanans og Jadduas Dage optegnedes Overhovederne for Fædrenehusene og Præsterne indtil Perseren Darius's Regering.
Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
23 Af Levis Efterkommere optegnedes Overhovederne for Fædrenehusene i Krønikebogen ned til Johanans, Eljasjibs Søns, Dage.
Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
24 Og Leviternes Overhoveder var: Hasjabja, Sjerebja, Jesua, Binnuj, Kadmiel og deres Brødre, der stod over for dem for at synge Lovsangen og Takkesangen efter den Guds Mand Davids Bud, den ene Afdeling efter den anden;
Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
25 og Mattanja, Bakbukja og Obadja, Mesjullam, Talmon og Akkub var Dørvogtere og holdt Vagt ved Portenes Forraadskamre.
Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
26 Disse var Overhoveder paa Jojakims Tid, en Søn af Jesua, en Søn af Jozadak, og paa Statholderen Nehemias's og Præsten Ezra den Skriftlærdes Tid.
Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
27 Da Jerusalems Mur skulde indvies, opsøgte man Leviterne alle Vegne, hvor de boede, og bragte dem til Jerusalem, for at de skulde fejre Indvielsen med Fryd og Takkesang, med Sang, Cymbler, Harper og Citre.
A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
28 Da samledes Sangerne fra Egnen om Jerusalem og fra Netofatiternes Landsbyer,
Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
29 fra Bet-Gilgal, fra Gebas og Azmavets Marker; thi Sangerne havde bygget sig Landsbyer rundt om Jerusalem.
daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
30 Da Præsterne og Leviterne havde renset sig, rensede de Folket, Portene og Muren.
Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
31 Saa lod jeg Judas Øverster stige op paa Muren og opstillede to store Lovprisningstog. Det ene drog til højre oven paa Muren ad Møgporten til,
Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
32 og med det fulgte Hosjaja og den ene Halvdel af Judas Øverster;
Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
33 dernæst nogle af Præsterne med Trompeter, Azarja, Ezra, Mesjullam,
tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
34 Juda, Benjamin, Sjemaja og Jirmeja;
Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
35 endvidere Zekarja, en Søn af Jonatan, en Søn af Sjemaja, en Søn af Mattanja, en Søn af Mika, en Søn af Zakkur, en Søn af Asaf,
da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
36 og hans Brødre Sjemaja, Azar'el, Milalaj, Gilalaj, Ma'aj, Netan'el, Juda, Hanani med den Guds Mand Davids Musikinstrumenter, med Ezra den Skriftlærde i Spidsen;
da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
37 og de gik over Kildeporten; derpaa gik de lige ud op ad Trinene til Davidsbyen, ad Opgangen paa Muren oven for Davids Palads hen til Vandporten mod Øst.
A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
38 Det andet Lovprisningstog, hvor jeg og den anden Halvdel af Folkets Øverster var med, drog til venstre oven paa Muren, over Ovntaarnet til den brede Mur
Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
39 og videre over Efraimsporten, den gamle Port, Fiskeporten, Hanan'eltaarnet og Meataarnet til Faareporten og stillede sig op i Fængselsporten.
bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
40 Derpaa stillede de to Lovprisningstog sig op i Guds Hus, jeg sammen med Halvdelen af Øversterne
Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
41 og Præsterne Eljakim, Ma'aseja, Minjamin, Mika, Eljoenaj, Zekarja, Hananja med Trompeter,
da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
42 endvidere Ma'aseja, Sjemaja, El'azar, Uzzi, Johanan, Malkija, Elam og Ezer. Og Sangerne stemte i, ledede af Jizraja.
haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
43 Paa den Dag ofrede de store Slagtofre og var glade, thi Gud havde bragt dem stor Glæde; ogsaa Kvinderne og Børnene var glade; og Glæden i Jerusalem hørtes langt bort.
A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
44 Paa den Dag indsattes der Mænd til at have Tilsyn med de Kamre, der brugtes til Forraadene, Offerydelserne, Førstegrøden og Tienden, for i dem at opsamle de i Loven foreskrevne Afgifter til Præsterne og Leviterne fra de forskellige Bymarker, thi Juda glædede sig over Præsterne og Leviterne, der gjorde Tjeneste;
A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
45 og disse tog Vare paa, hvad der var at varetage for deres Gud og ved Renselsen, ligesom ogsaa Sangerne og Dørvogterne gjorde deres Gerning efter Davids og hans Søn Salomos Bud.
Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
46 Thi allerede paa Davids Tid var Asaf Leder for Sangerne og for Lov— og Takkesangene til Gud.
Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
47 Hele Israel gav paa Zerubbabels og Nehemias's Tid Afgifter til Sangerne og Dørvogterne, efter som det krævedes Dag for Dag; og de gav Leviterne Helliggaver, og Leviterne gav Arons Sønner Helliggaver.
Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.