< Matthæus 19 >

1 Og det skete, da Jesus havde fuldendt disse Ord, drog han bort fra Galilæa og kom til Judæas Egne, hinsides Jordan.
Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun.
2 Og store Skarer fulgte ham, og han helbredte dem der.
Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.
3 Og Farisæerne kom til ham, fristede ham og sagde: „Er det tilladt at skille sig fra sin Hustru af hvilken som helst Grund?‟
Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, ''Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?''
4 Men han svarede og sagde: „Have I ikke læst, at Skaberen fra Begyndelsen skabte dem som Mand og Kvinde
Yesu ya amsa ya ce, ''Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
5 og sagde: „Derfor skal en Mand forlade sin Fader og sin Moder og holde sig til sin Hustru, og de to skulle blive til eet Kød?‟
Shi wanda ya yi su kuma ya ce, “Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?”
6 Saaledes ere de ikke længer to, men eet Kød. Derfor, hvad Gud har sammenføjet, maa et Menneske ikke adskille.‟
Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba.''
7 De sige til ham: „Hvorfor bød da Moses at give et Skilsmissebrev og skille sig fra hende?‟
Sai suka ce masa, ''To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?''
8 Han siger til dem: „Moses tilstedte eder at skille eder fra eders Hustruer for eders Hjerters Haardheds Skyld; men fra Begyndelsen har det ikke været saaledes.
Sai ya ce masu, ''Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba.
9 Men jeg siger eder, at den, som skiller sig fra sin Hustru, naar det ikke er for Hors Skyld, og tager en anden til Ægte, han bedriver Hor; og den, som tager en fraskilt Hustru til Ægte, han bedriver Hor.‟
Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina.''
10 Hans Disciple sige til ham: „Staar Mandens Sag med Hustruen saaledes, da er det ikke godt at gifte sig.‟
Almajiran suka ce wa Yesu, ''Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba.''
11 Men han sagde til dem: „Ikke alle rumme dette Ord, men de, hvem det er givet:
Amma Yesu yace masu, ''Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta.
12 Thi der er Gildinger, som ere fødte saaledes fra Moders Liv; og der er Gildinger, som ere gildede af Mennesker; og der er Gildinger, som have gildet sig selv for Himmeriges Riges Skyld. Den, som kan rumme det, han rumme det!‟
Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba.''
13 Da blev der baaret smaa Børn til ham, for at han skulde lægge Hænderne paa dem og bede; men Disciplene truede dem.
Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su.
14 Da sagde Jesus: „Lader de smaa Børn komme, og formener dem ikke at komme til mig; thi Himmeriges Rige hører saadanne til.‟
Amma Yesu ya ce masu, ''Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne.''
15 Og han lagde Hænderne paa dem, og han drog derfra.
Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
16 Og se, en kom til ham og sagde: „Mester! hvad godt skal jeg gøre, for at jeg kan faa et evigt Liv?‟ (aiōnios g166)
Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, ''Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?'' (aiōnios g166)
17 Men han sagde til ham: „Hvorfor spørger du mig om det gode? Een er den gode. Men vil du indgaa til Livet, da hold Budene!‟
Yesu ya ce masa, ''Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin.''
18 Han siger til ham: „Hvilke?‟ Men Jesus sagde: „Dette: Du maa ikke slaa ihjel; du maa ikke bedrive Hor; du maa ikke stjæle; du maa ikke sige falsk Vidnesbyrd;
Mutumin ya ce masa, ''Wadanne dokokin?'' Yesu ya ce masa, ''Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur,
19 ær din Fader og din Moder, og: Du skal elske din Næste som dig selv.‟
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.''
20 Den unge Mand siger til ham: „Det har jeg holdt alt sammen; hvad fattes mig endnu?‟
Saurayin nan ya ce masa, ''Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?''
21 Jesus sagde til ham: „Vil du være fuldkommen, da gaa bort, sælg, hvad du ejer, og giv det til fattige, saa skal du have en Skat i Himmelen; og kom saa og følg mig!‟
Yesu ya ce masa, ''Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni.''
22 Men da den unge Mand hørte det Ord, gik han bedrøvet bort; thi han havde meget Gods.
Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
23 Men Jesus sagde til sine Disciple: „Sandelig siger jeg eder: En rig kommer vanskeligt ind i Himmeriges Rige.
Yesu ya ce wa almajiransa, ''Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama.
24 Atter siger jeg eder: Det er lettere for en Kamel at gaa igennem et Naaleøje end for en rig at gaa ind i Guds Rige.‟
Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''
25 Men da Disciplene hørte dette, forfærdedes de saare og sagde: „Hvem kan da blive frelst?‟
Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, ''Wanene zai sami ceto?''
26 Men Jesus saa paa dem og sagde: „For Mennesker er dette umuligt, men for Gud ere alle Ting mulige.‟
Yesu ya dube su, ya ce, ''A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne.''
27 Da svarede Peter og sagde til ham: „Se, vi have forladt alle Ting og fulgt dig; hvad skulle da vi have?‟
Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, ''Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?''
28 Men Jesus sagde til dem: „Sandelig siger jeg eder, at i Igenfødelsen, naar Menneskesønnen sidder paa sin Herligheds Trone, skulle ogsaa I, som have fulgt mig, sidde paa tolv Troner og dømme Israels tolv Stammer.
Yesu ya ce masu, ''Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
29 Og hver, som har forladt Hus eller Brødre eller Søstre eller Fader eller Moder eller Hustru eller Børn eller Marker for mit Navns Skyld, skal faa det mange Fold igen og arve et evigt Liv. (aiōnios g166)
Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. (aiōnios g166)
30 Men mange af de første skulle blive de sidste, og af de sidste de første.
Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.

< Matthæus 19 >