< Malakias 2 >

1 Og nu udgaar følgende Paabud til eder, I Præster:
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 Hvis I ikke adlyder og lægger eder paa Sinde at holde mit Navn i Ære, siger Hærskarers HERRE, saa sender jeg Forbandelse over eder og vender eders Velsignelse til Forbandelse, ja til Forbandelse, fordi I ikke lægger eder det paa Sinde.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Se, jeg afhugger Armen paa eder og kaster Skarn i Ansigtet paa eder, Skarnet fra eders Højtider, og eders Ofre oven i Købet;
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 og I skal kende, at jeg har sendt eder dette Paabud, fordi jeg har en Pagt med Levi, siger Hærskarers HERRE.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 Min Pagt med ham var, at jeg skulde give ham Liv og Fred, og han skulde frygte mig og bæve for mit Navn;
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 Sandheds Lære var i hans Mund, Svig fandtes ikke paa hans Læber; i Fred og Sanddruhed vandrede han med mig, og mange holdt han fra Brøde.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 Thi Præstens Læber vogter paa Kundskab, og Vejledning søger man af hans Mund; thi han er Hærskarers HERRES Sendebud.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 Men I veg bort fra Vejen; mange har I bragt til Fald ved eders Vejledning, Levis Pagt har I ødelagt, siger Hærskarers HERRE.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Derfor har jeg ogsaa gjort eder ringeagtede og oversete af alt Folket, fordi I ikke tager Vare paa mine Veje eller bryder eder om Loven.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 Har vi ikke alle en og samme Fader, er det ikke en og samme Gud, som har skabt os? Hvorfor er vi da troløse mod hverandre, saa vi vanhelliger vore Fædres Pagt?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Juda er troløst, og Vederstyggelighed øves i Israel og Jerusalem; thi Juda vanhelliger den Helligdom, HERREN elsker, og tager en fremmed Guds Datter til Ægte.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 HERREN unddrage den Mand, som gør sligt, en til at vaage og svare i Jakobs Telte og en til at frembære Offergave for Hærskarers HERRE!
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 Og for det andet gør I dette: I hyller HERRENS Alter i Taarer, Graad og Klage, saa han ikke mere vender sig til Offergaven eller med Glæde modtager Gaver af eders Haand.
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 Og I spørger: »Hvorfor?« Fordi HERREN var Vidne mellem dig og din Ungdomshustru, mod hvem du har været troløs, skønt hun hører til dit Folk og deler din Tro.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 Saaledes gør ingen, saa længe der er Aand i ham. Hvorledes har det sig med ham? Han ønsker Afkom for Gud. Saa tag Vare paa eders Aand, og ingen være troløs imod sin Ungdomshustru!
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 Thi jeg hader Skilsmisse, siger HERREN, Israels Gud, og at man hyller sin Klædning i Uret, siger Hærskarers HERRE. Saa tag eder i Vare for eders Aands Skyld og vær ikke troløse!
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 I trætter HERREN med eders Ord. Og I spørger: »Hvorved trætter vi?« Ved at sige: »Enhver som gør ondt, er god i HERRENS Øjne; i dem har han Behag; hvor er ellers Dommens Gud?«
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”

< Malakias 2 >