< 3 Mosebog 21 >
1 Og HERREN sagde til Moses: Tal til Præsterne, Arons Sønner, og sig til dem: Præsten maa ikke gøre sig uren ved Lig blandt sin Slægt,
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
2 medmindre det er hans nærmeste kødelige Slægtninge, hans Moder eller Fader, hans Søn eller Datter, hans Broder
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 eller Søster, for saa vidt hun var Jomfru og endnu hørte til hans Familie og ikke var gift; i saa Fald maa han gøre sig uren ved hende;
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
4 men han maa ikke gøre sig uren ved hende, naar hun var gift med en Mand af hans Slægt, og saaledes paadrage sig Vanhelligelse.
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
5 De maa ikke klippe sig en skaldet Plet paa deres Hoved, ikke studse deres Skæg eller gøre Indsnit i deres Legeme.
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
6 Hellige skal de være for deres Gud og maa ikke vanhellige deres Guds Navn, thi de frembærer HERRENS Ildofre, deres Guds Spise; derfor skal de være hellige.
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
7 En Horkvinde og en skændet Kvinde maa de ikke ægte; heller ikke en Kvinde, der er forstødt af sin Mand, maa de ægte; thi han er helliget sin Gud.
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
8 Du skal regne ham for hellig, thi han frembærer din Guds Spise; han skal være dig hellig, thi hellig er jeg HERREN, som helliger dem.
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 Naar en Præstedatter vanhelliger sig ved at bedrive Hor, da vanhelliger hun sin Fader; hun skal brændes paa Baal.
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
10 Den Præst, der er den ypperste blandt sine Brødre, han, over hvis Hoved Salveolien udgydes, og som indsættes ved at iføres Klæderne, maa hverken lade sit Hovedhaar vokse frit eller sønderrive sine Klæder.
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
11 Han maa ikke gaa hen til noget som helst Lig, end ikke ved sin Fader eller Moder maa han gøre sig uren.
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
12 Han maa ikke forlade Helligdommen for ikke at vanhellige sin Guds Helligdom, thi hans Guds Salveolies Vielse er paa ham; jeg er HERREN!
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
13 Han skal ægte en Kvinde, der er Jomfru;
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
14 en Enke, en forstødt, en skændet, en Horkvinde maa han ikke ægte, kun en Jomfru af sin Slægt maa han tage til Hustru,
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
15 for at han ikke skal vanhellige sit Afkom blandt sin Slægt; thi jeg er HERREN, som helliger ham.
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
16 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Tal til Aron og sig: Ingen af dit Afkom i de kommende Slægter, som har en Legemsfejl, maa træde frem for at frembære sin Guds Spise,
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
18 det maa ingen, som har en Legemsfejl, hverken en blind eller en halt eller en med vansiret Ansigt eller for lang en Legemsdel
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
19 eller med Brud paa Ben eller Arm
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
20 eller en pukkelrygget eller en med Tæring eller en, der har Pletter i Øjnene eller lider af Skab eller Ringorm eller har svulne Testikler.
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
21 Af Præsten Arons Efterkommere maa ingen, som har en Legemsfejl, nærme sig for at frembære HERRENS Ildofre; han har en Legemsfejl, han maa ikke nærme sig for at frembære sin Guds Spise.
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
22 Han maa vel spise sin Guds Spise, baade det, som er højhelligt, og det, som er helligt,
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
23 men til Forhænget maa han ikke komme, og Alteret maa han ikke nærme sig, thi han har en Legemsfejl og maa ikke vanhellige mine hellige Ting; thi jeg er HERREN, som helliger dem.
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
24 Og Moses talte saaledes til Aron og hans Sønner og alle Israeliterne.
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.