< Klagesangene 3 >

1 Jeg er den, der saa nød ved hans vredes ris,
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 mig har han ført og ledt i det tykkeste Mulm,
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 ja, Haanden vender han mod mig Dagen lang.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Mit Kød og min Hud har han opslidt, brudt mine Ben,
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 han mured mig inde, omgav mig med Galde og Møje,
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 lod mig bo i Mørke som de, der for længst er døde.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Han har spærret mig inde og lagt mig i tunge Lænker.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Om jeg end raaber og skriger, min Bøn er stængt ude.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Han spærred mine Veje med Kvader, gjorde Stierne krøge.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Han blev mig en lurende Bjørn, en Løve i Baghold;
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 han ledte mig vild, rev mig sønder og lagde mig øde;
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 han spændte sin Bue; lod mig være Skive for Pilen.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Han sendte sit Koggers Sønner i Nyrerne paa mig;
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 hvert Folk lo mig ud og smæded mig Dagen lang,
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 med bittert mætted han mig, gav mig Malurt at drikke.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Mine Tænder lod han bide i Flint, han traadte mig i Støvet;
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 han skilte min Sjæl fra Freden, jeg glemte Lykken
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 og sagde: »Min Livskraft, mit Haab til HERREN er ude.«
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 At mindes min Vaande og Flakken er Malurt og Galde;
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 min Sjæl, den mindes det grant, den grubler betynget.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Det lægger jeg mig paa Sinde, derfor vil jeg haabe:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 HERRENS Miskundhed er ikke til Ende, ikke brugt op,
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 hans Naade er ny hver Morgen, hans Trofasthed stor.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Min Del er HERREN, (siger min Sjæl, ) derfor haaber jeg paa ham.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Dem, der bier paa HERREN, er han god, den Sjæl, der ham søger;
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 det er godt at haabe i Stilhed paa HERRENS Frelse,
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 godt for en Mand, at han bærer Aag i sin Ungdom.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Han sidde ensom og tavs, naar han lægger det paa ham;
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 han trykke sin Mund mod Støvet, maaske er der Haab,
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 række Kind til den, der slaar ham, mættes med Haan.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Thi Herren bortstøder ikke for evigt,
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 har han voldt Kvide, saa ynkes han, stor er hans Naade;
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 ej af Hjertet plager og piner han Menneskens Børn.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Naar Landets Fanger til Hobe trædes under Fod,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 naar Mandens Ret for den Højestes Aasyn bøjes,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 naar en Mand lider Uret i sin Sag — mon Herren ej ser det?
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Hvo taler vel, saa det sker, om ej Herren byder?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Kommer ikke baade ondt og godt fra den Højestes Mund?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Over hvad skal den levende sukke? Hver over sin Synd!
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Lad os ransage, granske vore Veje og vende os til HERREN,
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 løfte Hænder og Hjerte til Gud i Himlen;
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 vi syndede og stod imod, du tilgav ikke,
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 men hylled dig i Vrede, forfulgte os, dræbte uden Skaansel,
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 hylled dig i Skyer, saa Bønnen ej naaede frem;
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 til Skarn og til Udskud har du gjort os midt iblandt Folkene.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 De opspærred Munden imod os, alle vore Fjender.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Vor Lod blev Gru og Grav og Sammenbruds Øde;
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Vandstrømme græder mit Øje, mit Folk brød sammen.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Hvileløst strømmer mit Øje, det kender ej Ro,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 før HERREN skuer ned fra Himlen, før han ser til.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Synet af Byens Døtre piner min Sjæl.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Jeg joges som en Fugl af Fjender, hvis Had var grundløst,
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 de spærred mig inde i en Grube, de stenede mig;
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Vand strømmed over mit Hoved, jeg tænkte: »Fortabt!«
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Dit Navn paakaldte jeg, HERRE, fra Grubens Dyb;
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 du hørte min Røst: »O, gør dig ej døv for mit Skrig!«
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Nær var du, den Dag jeg kaldte, du sagde: »Frygt ikke!«
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Du førte min Sag, o HERRE, genløste mit Liv;
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 HERRE, du ser, jeg lider Uret, skaf mig min Ret!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Al deres Hævnlyst ser du, alle deres Rænker,
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 du hører deres Smædeord, HERRE, deres Rænker imod mig,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 mine Fjenders Tale og Tanker imod mig bestandig.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Se dem, naar de sidder eller staar, deres Nidvise er jeg.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Dem vil du gengælde, HERRE, deres Hænders Gerning,
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 gør deres Hjerte forhærdet — din Forbandelse over dem! —
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 forfølg dem i Vrede, udryd dem under din Himmel.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Klagesangene 3 >