< Job 38 >

1 Saa svarede HERREN Job ud fra Stormvejret og sagde:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Hvem fordunkler mit Raad med Ord, som er uden Mening?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Omgjord som en Mand dine Lænder, jeg vil spørge, og du skal lære mig!
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Hvor var du, da jeg grundede Jorden? Sig frem, om du har nogen Indsigt!
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Hvem bestemte dens Maal — du kender det jo — hvem spændte Maalesnor ud derover?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Hvorpaa blev dens Støtter sænket, hvem lagde dens Hjørnesten,
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 mens Morgenstjernerne jubled til Hobe, og alle Gudssønner raabte af Glæde?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Hvem stængte for Havet med Porte, dengang det brusende udgik af Moders Skød,
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 dengang jeg gav det Skyen til Klædning og Taagemulm til Svøb,
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 dengang jeg brød det en Grænse og indsatte Portslaa og Døre
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 og sagde: »Hertil og ikke længer! Her standse dine stolte Vover!«
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Har du nogen Sinde kaldt Morgenen frem, ladet Morgenrøden vide sit Sted,
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 saa den greb om Jordens Flige og gudløse rystedes bort,
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 saa den dannedes til som Ler under Segl, fik Farve, som var den en Klædning?
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 De gudløses Lys toges fra dem, den løftede Arm blev knust.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Har du mon været ved Havets Kilder, har du mon vandret paa Dybets Bund?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Mon Dødens Porte har vist sig for dig, skued du Mulmets Porte?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Saa du ud over Jordens Vidder? Sig frem, om du ved, hvor stor den er!
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Hvor er Vejen til Lysets Bolig, og hvor har Mørket mon hjemme,
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 saa du kunde hente det til dets Rige og bringe det hen paa Vej til dets Bolig?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Du ved det, du blev jo født dengang, dine Dages Tal er jo stort!
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Har du været, hvor Sneen gemmes, og skuet, hvor Hagelen vogtes,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 den, jeg gemmer til Trængselens Tid, til Kampens og Krigens Dag?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Hvor er Vejen did, hvor Lyset deler sig, hvor Østenvinden spreder sig ud over Jorden?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Hvem aabnede Regnen en Rende og Tordenens Lyn en Vej
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 for at væde folketomt Land, Ørkenen, hvor ingen bor,
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 for at kvæge Øde og Ødemark og fremkalde Urter i Ørkenen?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Har Regnen mon en Fader, hvem avlede Duggens Draaber?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Af hvilket Skød kom Isen vel frem, hvem fødte mon Himlens Rim?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 Vandet størkner som Sten, Dybets Flade trækker sig sammen.
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Knytter du Syvstjernens Baand, kan du løse Orions Lænker?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Lader du Aftenstjernen gaa op i Tide, leder du Bjørnen med Unger?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Kender du Himmelens Love, fastsætter du dens Magt over Jorden?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Kan du løfte Røsten til Sky, saa Vandskyl adlyder dig?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Sender du Lynene ud, saa de gaar, og svarer de dig: »Her er vi!«
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Hvem lagde Visdom i sorte Skyer, hvem gav Luftsynet Kløgt?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Hvem er saa viis, at han tæller Skyerne, hvem hælder Himmelens Vandsække om,
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 naar Jorden ligger i Ælte, og Leret klumper sig sammen?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Jager du Rov til Løvinden, stiller du Ungløvers Hunger,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 naar de dukker sig i deres Huler; ligger paa Lur i Krat?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Hvem skaffer Ravnen Æde, naar Ungerne skriger til Gud og flakker om uden Føde?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?

< Job 38 >