< Job 31 >

1 Jeg sluttede en Pagt med mit Øje om ikke at se paa en Jomfru;
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 hvad var ellers min Lod fra Gud hist oppe, den Arv, den Almægtige gav fra det høje?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Har ikke den lovløse Vanheld i Vente, Udaadsmændene Modgang?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Ser han ej mine Veje og tæller alle mine Skridt?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Har jeg holdt til med Løgn, og hasted min Fod til Svig —
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 paa Rettens Vægtskaal veje han mig, saa Gud kan kende min Uskyld —
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 er mit Skridt bøjet af fra Vejen, og har mit Hjerte fulgt mine Øjne, hang noget ved mine Hænder,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 da gid jeg maa saa og en anden fortære, og hvad jeg planted, oprykkes med Rode!
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Blev jeg en Daare paa Grund af en Kvinde, og har jeg luret ved Næstens Dør,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 saa dreje min Hustru Kværn for en anden, og andre bøje sig over hende!
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Thi sligt var Skændselsdaad, Brøde, der drages for Retten,
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 ja, Ild, der æder til Afgrunden og sætter hele min Høst i Brand!
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Har jeg ringeagtet min Træls og min Trælkvindes Ret, naar de trættede med mig,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 hvad skulde jeg da gøre, naar Gud stod op, hvad skulde jeg svare, naar han saa efter?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Har ikke min Skaber skabt ham i Moders Skød, har en og samme ej dannet os begge i Moders Liv?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Har jeg afslaaet ringes Ønske, ladet Enkens Øjne vansmægte,
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 var jeg ene om at spise mit Brød, har den faderløse ej spist deraf —
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 nej, fra Barnsben fostred jeg ham som en Fader, jeg ledede hende fra min Moders Skød.
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Har jeg set en Stakkel blottet for Klæder, en fattig savne et Tæppe —
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 visselig nej, hans Hofter velsigned mig, naar han varmed sig i Uld af mine Lam.
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Har jeg løftet min Baand mod en faderløs, fordi jeg var vis paa Medhold i Retten,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 saa falde min Skulder fra Nakken, saa rykkes min Arm af Led!
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Thi Guds Rædsel var kommet over mig, og naar han rejste sig, magted jeg intet!
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Har jeg slaaet min Lid til Guld, kaldt det rene Guld min Fortrøstning,
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 var det min Glæde, at Rigdommen voksed, og at min Haand fik sanket saa meget,
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 saa jeg, hvorledes Sollyset straaled, eller den herligt skridende Maane,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 og lod mit Hjerte sig daare i Løn, saa jeg hylded dem med Kys paa min Haand —
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 ogsaa det var Brøde, der drages for Retten, thi da fornægted jeg Gud hist oppe.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Var min Avindsmands Fald min Glæd jubled jeg, naar han ramtes af Vanheld —
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 nej, jeg tillod ikke min Gane at synde, saa jeg bandende kræved hans Sjæl.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Har min Husfælle ej maattet sige: »Hvem mættedes ej af Kød fra hans Bord« —
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 nej, den fremmede laa ej ude om Natten, jeg aabned min Dør for Vandringsmænd.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Har jeg skjult mine Synder, som Mennesker gør, saa jeg dulgte min Brøde i Brystet
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 af Frygt for den store Hob, af Angst for Stamfrænders Ringeagt, saa jeg blev inden Døre i Stilhed! —
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Ak, var der dog en, der hørte paa mig! Her er mit Bomærke — lad den Almægtige svare! Havde jeg blot min Modparts Indlæg!
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Sandelig, tog jeg det paa min Skulder, kransed mit Hoved dermed som en Krone,
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 svared ham for hvert eneste Skridt og mødte ham som en Fyrste.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Har min Mark maattet skrige over mig og alle Furerne græde,
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 har jeg tæret dens Kraft uden Vederlag, udslukt dens Ejeres Liv,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 saa gro der Tjørn for Hvede og Ukrudt i Stedet for Byg! Her ender Jobs Ord.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >