< Job 29 >

1 Og Job vedblev at fremsætte sit Tankesprog:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 Ak, havde jeg det som tilforn, som dengang Gud tog sig af mig,
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 da hans Lampe lyste over mit Hoved, og jeg ved hans Lys vandt frem i Mørke,
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 som i mine modne Aar, da Guds Fortrolighed var over mit Telt,
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 da den Almægtige end var hos mig og mine Drenge var om mig,
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 da mine Fødder vaded i Fløde, og Olie strømmede, hvor jeg stod,
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 da jeg gik ud til Byens Port og rejste mit Sæde paa Torvet.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 Naar Ungdommen saa mig, gemte den sig, Oldinge rejste sig op og stod,
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 Høvdinger standsed i Talen og lagde Haand paa Mund,
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 Stormænds Røst forstummed, deres Tunge klæbed til Ganen;
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 Øret hørte og priste mig lykkelig, Øjet saa og tilkendte mig Ære.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 Thi jeg redded den arme, der skreg om Hjælp, den faderløse, der savned en Hjælper;
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 den, det gik skævt, velsignede mig, jeg frydede Enkens Hjerte;
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 jeg klædte mig i Retfærd, og den i mig, i Ret som Kappe og Hovedbind.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Jeg var den blindes Øje, jeg var den lammes Fod;
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 jeg var de fattiges Fader, udreded den mig ukendtes Sag;
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 den lovløses Tænder brød jeg, rev Byttet ud af hans Gab.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Saa tænkte jeg da: »Jeg skal dø i min Rede, leve saa længe som Føniksfuglen;
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 min Rod kan Vand komme til, Duggen har Nattely i mine Grene;
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 min Ære er altid ny, min Bue er altid ung i min Haand!«
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Mig hørte de paa og bied, var tavse, mens jeg gav Raad;
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 ingen tog Ordet, naar jeg havde talt, mine Ord faldt kvægende paa dem;
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 de bied paa mig som paa Regn, spærred Munden op efter Vaarregn.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Mistrøstige smilte jeg til, mit Aasyns Lys fik de ej til at svinde.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Vejen valgte jeg for dem og sad som Høvding, troned som Konge blandt Hærmænd, som den, der gav sørgende Trøst.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >