< Job 21 >
1 Saa tog Job til Orde og svarede:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hør dog, hør mine Ord, lad det være Trøsten, I giver!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Find jer nu i, at jeg taler, siden kan I jo haane!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Gælder min Klage Mennesker? Hvi skulde jeg ej være utaalmodig?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Vend jer til mig og stivn af Rædsel, læg Haand paa Mund!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Jeg gruer, naar jeg tænker derpaa, mit Legeme gribes af Skælven:
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 De gudløse, hvorfor lever de, bliver gamle, ja vokser i Kraft?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Deres Æt har de blivende hos sig, deres Afkom for deres Øjne;
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 deres Huse er sikre mod Rædsler, Guds Svøbe rammer dem ikke;
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 ej springer deres Tyr forgæves, Koen kælver, den kaster ikke;
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 de slipper deres Drenge ud som Faar, deres Børneflok boltrer sig ret;
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 de synger til Pauke og Citer, er glade til Fløjtens Toner;
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 de lever deres Dage i Lykke og synker med Fred i Dødsriget, (Sheol )
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
14 skønt de siger til Gud: »Gaa fra os, at kende dine Veje er ikke vor Lyst!
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Den Almægtige? Hvad han? Skal vi tjene ham? Hvad Gavn at banke paa hos ham?«
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Er ej deres Lykke i deres Haand og gudløses Raad ham fjernt?
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Naar gaar de gudløses Lampe ud og naar kommer Ulykken over dem? Naar deler han Loddet ud i sin Vrede,
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 saa de bliver som Straa for Vinden, som Avner, Storm fører bort?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Gemmer Gud hans Ulykkeslod til hans Børn? Ham selv gengælde han, saa han mærker det,
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 lad ham selv faa sit Vanheld at se, den Almægtiges Vrede at drikke!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Thi hvad bryder han sig siden om sit Hus, naar hans Maaneders Tal er udrundet?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Kan man vel tage Gud i Skole, ham, som dømmer de højeste Væsner?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 En dør jo paa Lykkens Tinde, helt tryg og saa helt uden Sorger:
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 hans Spande er fulde af Mælk, hans Knogler af saftig Marv;
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 med bitter Sjæl dør en anden og har aldrig nydt nogen Lykke;
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 de lægger sig begge i Jorden, og begge dækkes af Orme!
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Se, jeg kender saa vel eders Tanker og de Rænker, I spinder imod mig,
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 naar I siger: »Hvor er Stormandens Hus og det Telt, hvor de gudløse bor?«
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Har I aldrig spurgt de berejste og godkendt deres Beviser:
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Den onde skaanes paa Ulykkens Dag og frelses paa Vredens Dag.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Hvem foreholder ham vel hans Færd, gengælder ham, hvad han gør?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Til Graven bæres han hen, ved hans Gravhøj holdes der Vagt;
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 i Dalbunden hviler han sødt, Alverden følger saa efter, en Flok uden Tal gik forud for ham.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Hvor tom er den Trøst, som I giver! Eders Svar — kun Svig er tilbage!
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”