< Hebræerne 12 >
1 Derfor lader ogsaa os, efterdi vi have saa stor en Sky af Vidner omkring os, aflægge enhver Byrde og Synden, som lettelig hilder os, og med Udholdenhed gennemløbe den foran os liggende Bane,
Da shike muna kewaye da wannan irin kasaitaccen taro na shaidu, sai mu watsar da dukkan abubuwan dake nawaita mana da kuma zunubin da zai saurin makale ma na. Bari a cikin hakuri mu yi tseren da ke gabanmu.
2 idet vi se hen til Troens Begynder og Fuldender, Jesus, som for den foran ham liggende Glædes Skyld udholdt et Kors, idet han ringeagtede Skændselen, og som har taget Sæde paa højre Side af Guds Trone.
Bari mu kafa idonmu ga Yesu, wanda shine mafarin bangaskiyarmu da cikarta. Wanda sabili da murnar da a ka sa a gabansa ya jimre giciye, ya kuma yi watsi da kunyarsa, wanda kuma ya zauna a hannun dama na kursiyin Allah.
3 Ja, tænker paa ham, som har udholdt en saadan Modsigelse imod sig af Syndere, for at I ikke skulle blive trætte og forsagte i eders Sjæle.
Ku dube shi wanda ya jimre irin wannan adawa daga masu zunubi, domin kada ku gaji ko ku karai.
4 Endnu have I ikke staaet imod indtil Blodet i eders Kamp imod Synden,
Ba ku yi tsayayya ko jayayya da zunubi har ta kai ga zub da jininku ba tukunna. Kun kuma manta da gargadin da a ka yi maku a matsayin 'ya'ya:
5 og I have glemt Formaningen, der jo dog taler til eder som til Sønner: \x{201c}Min Søn! agt ikke Herrens Tugtelse ringe, vær heller ikke forsagt, naar du revses af ham;
''Dana, kada ka dauki horon Ubangiji da wasa, kadda kuma ka yi suwu lokacin da ka sami horonsa,''
6 thi hvem Herren elsker, den tugter han, og han slaar haardelig hver Søn, som han tager sig af.\x{201d}
Domin kuwa Ubangiji yana horon dukkan wadanda yake kauna, yana kuma hukunta duk wadanda ya karba.
7 Holder ud og lader eder tugte; Gud handler med eder som med Sønner; thi hvem er den Søn, som Faderen ikke tugter?
Ku daure wahala a matsayin horo. Allah yana yi da ku kamar 'ya'yansa, domin kuwa wanne da ne wanda ubansa bazai yi masa horo ba?
8 Men dersom I ere uden Tugtelse, hvori alle have faaet Del, da ere I jo uægte og ikke Sønner.
Amma idan baku da horo kamar yadda sauran mutane ke da shi, kun zama shegu kenan ba 'ya'ya ba.
9 Fremdeles, vore kødelige Fædre havde vi til Optugtere, og vi følte Ærefrygt; skulde vi da ikke meget mere underordne os under Aandernes Fader og leve?
Hakannan kuma kamar yadda muke da iyaye a duniya wadanda suke yi mana horo, kuma muna basu daraja. To ba sai mu yiwa Ubanmu na Ruhaniya biyayya don mu rayu ba?
10 Thi hine tugtede os for nogle faa Dage efter deres Tykke, men han gør det til vort Gavn, for at vi skulle faa Del i hans Hellighed.
Ta wani fanni kuwa iyayenmu suna yi mana horo na kwanaki kadan bisa ga yadda suka ga ya dace, Amma Allah kuwa yana yi mana horo domin anfanin kanmu, domin kuma mu sami rabo daga cikin tsarkinsa.
11 Al Tugtelse synes vel, imedens den er nærværende, ikke at være til Glæde, men til Bedrøvelse; men siden giver den til Gengæld dem, som derved ere øvede, en Fredens Frugt i Retfærdighed.
Ba horon da ke da dadi a lokacin yinsa, amma sai zafi. Sai dai kuma bayan haka yakan haifar da 'ya'ya na ruhaniya da kuma adalci ga dukkan wadanda aka yi rainonsu a ciki.
12 Derfor, retter de slappede Hænder og de lammede Knæ,
Don haka sai ku karfafa hannayenku da ke reto, da kuma guwawunku da ke kaduwa.
13 og træder lige Spor med eders Fødder, for at ikke det lamme skal vrides af Led, men snarere helbredes.
Ku bi hanyoyi mikakku domin abin da ya gurgunce kada ya karye amma ya warke.
14 Stræber efter Fred med alle og efter Helliggørelsen, uden hvilken ingen skal se Herren;
Ku bidi salama da kowa, da kuma rayuwar tsarki wanda in ba tare da shi, babu wanda zai ga Allah.
15 og ser til, at ikke nogen gaar Glip af Guds Naade, at ikke nogen bitter Rod skyder op og gør Skade, og de mange smittes ved den;
Ku mai da hankali domin kada waninku ya rasa, alherin Allah, kuma kada wani tushe mai daci ya tsiro a cikinku har ya haifar da fitina, domin kada da dama daga cikinku su gurbata ta wurinsa.
16 at ikke nogen er en utugtig eller en vanhellig som Esau, der for een Ret Mad solgte sin Førstefødselsret.
Ku yi hankali kuma kada a sami mazinanci ko marar ibada a cikinku, kamar Isuwa, wanda sabili da abinci ya sayar da 'yancinsa na dan fari.
17 Thi I vide, at han ogsaa siden, da han ønskede at arve Velsignelsen, blev forkastet (thi han fandt ikke Rum for Omvendelse), omendskønt han begærede den med Taarer.
Kun kuwa san cewa sa'adda ya yi marmarin ya gaji albarka a gaba, an kishi, domin kuwa bai sami damar tuba ba, ko da shike ya nema har da hawaye.
18 I ere jo ikke komne til en haandgribelig og brændende Ild og til Mulm og Mørke og Uvejr,
Domin kuwa baku zo ga dusen da ake tabawa da hannu ba, dutse ne mai ci da wuta, da tukuki da bakin hayaki da hadari.
19 og ikke til Basunens Klang og til en talende Røst, hvorom de, der hørte den, bade, at der ikke mere maatte tales til dem.
Ba Ku zo ga karar kaho mai ban razana da murya mai firgitarwa ba, da masu sauraro suka yi roko kar su sake jinta.
20 Thi de kunde ikke bære det, som blev paabudt: \x{201c}Endog om et Dyr rører ved Bjerget, skal det stenes.\x{201d}
Don basu iya jimre abin da aka yi doka a kan saba: ''koma dabba ce ta taba dutsen, sai a jejjefe ta.''
21 Og — saa frygteligt var Synet — Moses sagde: \x{201c}Jeg er forfærdet og bæver.\x{201d}
Abin tsoro ne kuwa kwarai, har Musa yace, ''A tsoroce nake kwarai har na firgita.''
22 Men I ere komne til Zions Bjerg og til den levende Guds Stad, til det himmelske Jerusalem og til Englenes Titusinder i Højtidsskare
Maimakon haka kun zone ga Dutsen Sihiyona da kuma birni na Allah mai Rai, kuma na Urushalima ta Samniya, da kuma dubun dubban mala'iku cikin murna da farin ciki.
23 og til de førstefødtes Menighed, som ere indskrevne i Himlene, og til en Dommer, som er alles Gud, og til de fuldkommede retfærdiges Aander
Kun zo taro na dukkan 'ya'yan fari, rubuttatu a sama, kuma kun zo ga Allah wanda shine alkalin dukka, hakannan kuma zuwa ga ruhu na adalai wanda a ka rigaya aka tsarkake.
24 og til den nye Pagts Mellemmand, Jesus, og til Bestænkelsens Blod, som taler bedre end Abel.
Kun zo ga Yesu, wanda shine matsakancin sabon alkawari, kuma ga jinin yayyafawa da ke magana fiye da na jinin Habila.
25 Ser til, at I ikke bede eder fri for den, som taler. Thi naar de, som bade sig fri for ham, der talte sit Guddomsord paa Jorden, ikke undslap, da skulle vi det meget mindre, naar vi vende os bort fra ham, der taler fra Himlene,
Ku yi lura kada ku ki wannan da ke yi mu ku magana. Gama in har basu kubuta yayin da su ka yi jayayya da wanda ya yi mu su gargadi a duniya ba, balle ma mu ba za mu kubuta ba in mun ki wanda ke mana gargadi daga sama.
26 han, hvis Røst dengang rystede Jorden, men som nu har forjættet og sagt: \x{201c}Endnu een Gang vil jeg ryste, ikke alene Jorden, men ogsaa Himmelen.\x{201d}
A wani karo, muryar sa ta girgiza duniya. Amma yanzu yayi alkawari da cewa, ''Har'ila yau ba duniyar kadai zan girgiza ba, amma har da sammai.''
27 Men dette \x{201c}endnu een Gang\x{201d} giver til Kende, at de Ting, der rystes, skulle omskiftes, efterdi de ere skabte, for at de Ting, der ikke rystes, skulle blive.
Wannan kalma, ''Harl'ila yau,'' ta bayyana cirewar abubuwan nan da za su girgizu, wato abubuwan da a ka halitta, domin abubuwan da ba zasu girgizu ba su kasance.
28 Derfor, efterdi vi modtage et Rige, som ikke kan rystes, saa lader os være taknemmelige og derved tjene Gud til hans Velbehag, med Ængstelse og Frygt.
Don haka, samun mulkin da ba za ya girgizu ba, sai mu zama masu godiya, kuma a cikin wannan yanayi mu yi wa Allah sujada cikin daraja da tsaninin gimamawa.
29 Thi vor Gud er en fortærende Ild.
Domin kuwa Allahnmu wuta ne mai konewa.