< Hebræerne 12 >

1 Derfor lader ogsaa os, efterdi vi have saa stor en Sky af Vidner omkring os, aflægge enhver Byrde og Synden, som lettelig hilder os, og med Udholdenhed gennemløbe den foran os liggende Bane,
Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
2 idet vi se hen til Troens Begynder og Fuldender, Jesus, som for den foran ham liggende Glædes Skyld udholdt et Kors, idet han ringeagtede Skændselen, og som har taget Sæde paa højre Side af Guds Trone.
Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
3 Ja, tænker paa ham, som har udholdt en saadan Modsigelse imod sig af Syndere, for at I ikke skulle blive trætte og forsagte i eders Sjæle.
Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
4 Endnu have I ikke staaet imod indtil Blodet i eders Kamp imod Synden,
Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
5 og I have glemt Formaningen, der jo dog taler til eder som til Sønner: \x{201c}Min Søn! agt ikke Herrens Tugtelse ringe, vær heller ikke forsagt, naar du revses af ham;
Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
6 thi hvem Herren elsker, den tugter han, og han slaar haardelig hver Søn, som han tager sig af.\x{201d}
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
7 Holder ud og lader eder tugte; Gud handler med eder som med Sønner; thi hvem er den Søn, som Faderen ikke tugter?
Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
8 Men dersom I ere uden Tugtelse, hvori alle have faaet Del, da ere I jo uægte og ikke Sønner.
In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
9 Fremdeles, vore kødelige Fædre havde vi til Optugtere, og vi følte Ærefrygt; skulde vi da ikke meget mere underordne os under Aandernes Fader og leve?
Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
10 Thi hine tugtede os for nogle faa Dage efter deres Tykke, men han gør det til vort Gavn, for at vi skulle faa Del i hans Hellighed.
Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
11 Al Tugtelse synes vel, imedens den er nærværende, ikke at være til Glæde, men til Bedrøvelse; men siden giver den til Gengæld dem, som derved ere øvede, en Fredens Frugt i Retfærdighed.
Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
12 Derfor, retter de slappede Hænder og de lammede Knæ,
Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
13 og træder lige Spor med eders Fødder, for at ikke det lamme skal vrides af Led, men snarere helbredes.
“Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
14 Stræber efter Fred med alle og efter Helliggørelsen, uden hvilken ingen skal se Herren;
Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
15 og ser til, at ikke nogen gaar Glip af Guds Naade, at ikke nogen bitter Rod skyder op og gør Skade, og de mange smittes ved den;
Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
16 at ikke nogen er en utugtig eller en vanhellig som Esau, der for een Ret Mad solgte sin Førstefødselsret.
Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
17 Thi I vide, at han ogsaa siden, da han ønskede at arve Velsignelsen, blev forkastet (thi han fandt ikke Rum for Omvendelse), omendskønt han begærede den med Taarer.
Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
18 I ere jo ikke komne til en haandgribelig og brændende Ild og til Mulm og Mørke og Uvejr,
Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
19 og ikke til Basunens Klang og til en talende Røst, hvorom de, der hørte den, bade, at der ikke mere maatte tales til dem.
ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
20 Thi de kunde ikke bære det, som blev paabudt: \x{201c}Endog om et Dyr rører ved Bjerget, skal det stenes.\x{201d}
domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
21 Og — saa frygteligt var Synet — Moses sagde: \x{201c}Jeg er forfærdet og bæver.\x{201d}
Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
22 Men I ere komne til Zions Bjerg og til den levende Guds Stad, til det himmelske Jerusalem og til Englenes Titusinder i Højtidsskare
Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
23 og til de førstefødtes Menighed, som ere indskrevne i Himlene, og til en Dommer, som er alles Gud, og til de fuldkommede retfærdiges Aander
kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
24 og til den nye Pagts Mellemmand, Jesus, og til Bestænkelsens Blod, som taler bedre end Abel.
Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
25 Ser til, at I ikke bede eder fri for den, som taler. Thi naar de, som bade sig fri for ham, der talte sit Guddomsord paa Jorden, ikke undslap, da skulle vi det meget mindre, naar vi vende os bort fra ham, der taler fra Himlene,
Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
26 han, hvis Røst dengang rystede Jorden, men som nu har forjættet og sagt: \x{201c}Endnu een Gang vil jeg ryste, ikke alene Jorden, men ogsaa Himmelen.\x{201d}
A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
27 Men dette \x{201c}endnu een Gang\x{201d} giver til Kende, at de Ting, der rystes, skulle omskiftes, efterdi de ere skabte, for at de Ting, der ikke rystes, skulle blive.
Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
28 Derfor, efterdi vi modtage et Rige, som ikke kan rystes, saa lader os være taknemmelige og derved tjene Gud til hans Velbehag, med Ængstelse og Frygt.
Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
29 Thi vor Gud er en fortærende Ild.
gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”

< Hebræerne 12 >