< 1 Mosebog 8 >

1 Da ihukom Gud Noa og alle de vilde Dyr og Kvæget, som var hos ham i Arken; og Gud lod en Storm fare hen over Jorden, saa at Vandet begyndte at falde;
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 Verdensdybets Kilder og Himmelens Sluser lukkedes, Regnen fra Himmelen standsede,
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 og Vandet veg lidt efter lidt bort fra Jorden, og Vandet tog af efter de 150 Dages Forløb.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 Paa den syttende Dag i den syvende Maaned sad Arken fast paa Ararats Bjerge,
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 og Vandet vedblev at synke indtil den tiende Maaned, og paa den første Dag i denne Maaned dukkede Bjergenes Toppe frem.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 Da der var gaaet fyrretyve Dage: aabnede Noa den Luge, han havde lavet paa Arken,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 og sendte en Ravn ud; den fløj frem og tilbage, indtil Vandet var tørret bort fra Jorden.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 Da sendte han en Due ud for at se, om Vandet var sunket fra Jordens Overflade;
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 men Duen fandt intet Sted at sætte sin Fod og vendte tilbage til ham i Arken, fordi der endnu var Vand over hele Jorden; og han rakte Haanden ud og tog den ind i Arken til sig.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 Derpaa biede han yderligere syv Dage og sendte saa atter Duen ud fra Arken;
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 ved Aftenstid kom Duen tilbage til ham, og se, den havde et friskt Olieblad i Næbbet. Da skønnede Noa, at Vandet var svundet bort fra Jorden.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 Derpaa biede han syv Dage til, og da han saa sendte Duen ud, kom den ikke mere tilbage til ham.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 I Noas 601ste Leveaar paa den første Dag i den første Maaned var Vandet tørret bort fra Jorden. Da tog Noa Dækket af Arken, og da han saa sig om, se, da var Jordens Overflade tør.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 Paa den syv og tyvende Dag i den anden Maaned var Jorden tør.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 Da sagde Gud til Noa:
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 »Gaa ud af Arken med din Hustru, dine Sønner og dine Sønnekoner
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 og for alle Dyr, der er hos dig, alt Kød, Fugle, Kvæg og alt Kryb, der kryber paa Jorden, ud med dig, at de kan vrimle paa Jorden og blive frugtbare og mangfoldige paa Jorden!«
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 Da gik Noa ud med sine Sønner, sin Hustru og sine Sønnekoner;
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 og alle de vildtlevende Dyr, alt Kvæget, alle Fuglene og alt Krybet, der kryber paa Jorden, efter deres Slægter, gik ud af Arken.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 Derpaa byggede Noa HERREN et Alter og tog nogle af alle de rene Dyr og Fugle og ofrede Brændofre paa Alteret.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 Og da HERREN indaandede den liflige Duft, sagde han til sig selv: »Jeg vil aldrig mere forbande Jorden for Menneskenes Skyld, thi Menneskehjertets Higen er ond fra Ungdommen af, og jeg vil aldrig mere tilintetgøre alt, hvad der lever, saaledes som jeg nu har gjort!
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 Herefter skal, saa længe Jorden staar, Sæd og Høst, Kulde og Hede, Sommer og Vinter, Dag og Nat ikke ophøre!«
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”

< 1 Mosebog 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark