< 1 Mosebog 45 >
1 Da kunde Josef ikke længer beherske sig over for alle dem der stod hos ham, og han raabte »Lad alle gaa ud!« Saaledes var der ingen til Stede, da Josef gav sig til Kende for sine Brødre.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 Saa brast han i lydelig Graad, saa Ægypterne hørte det, og det spurgtes i Faraos Hus;
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 og Josef sagde til sine Brødre: »Jeg er Josef! Lever min Fader endnu?« Men hans Brødre kunde ikke svare ham, saa forfærdede var de for ham.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 Saa sagde Josef til sine Brødre: »Kom hen til mig!« Og da de kom derhen, sagde Josef: »Jeg er eders Broder Josef, som I solgte til Ægypten;
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 men I skal ikke græmme eder eller være forknytte, fordi I solgte mig herhen, thi Gud har sendt mig forud for eder for at opholde Liv;
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 i to Aar har der nu været Hungersnød i Landet, og fem Aar endnu skal der hverken pløjes eller høstes;
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 derfor sendte Gud mig forud for eder, for at I kan faa Efterkommere paa Jorden, og for at mange hos eder kan reddes og holdes i Live.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 Og nu, ikke I, men Gud har sendt mig hid, og han har gjort mig til Fader hos Farao og til Herre over hele hans Hus og til Hersker over hele Ægypten.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Skynd jer nu hjem til min Fader og sig til ham: Din Søn Josef lader sige: Gud har sat mig til Hersker over hele Ægypten; kom uden Tøven ned til mig
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 og tag Bolig i Gosens Land og bo i min Nærhed med dine Sønner og Sønnesønner, dit Smaakvæg og Hornkvæg og alt, hvad du ejer og har;
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 der vil jeg sørge for dit Underhold — thi Hungersnøden vil vare fem Aar endnu — for at ikke du, dit Hus eller nogen, der hører dig til, skal gaa til Grunde!
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 Nu ser I, ogsaa min Broder Benjamin, med egne Øjne, at det er mig, der taler til eder;
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 og I skal fortælle min Fader om al min Herlighed i Ægypten og om alt, hvad I har set, og saa skal I skynde eder at bringe min Fader herned.«
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 Saa faldt han grædende sin Broder Benjamin om Halsen, og Benjamin græd i hans Arme.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 Og han kyssede alle sine Brødre og græd ved deres Bryst; og nu kunde hans Brødre tale med ham.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 Men det spurgtes i Faraos Hus, at Josefs Brødre var kommet, og Farao og hans Tjenere glædede sig derover:
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 og Farao sagde til Josef: »Sig til dine Brødre: Saaledes skal I gøre: Læs eders Dyr og drag til Kana'ans Land,
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 hent eders Fader og eders Familier og kom hid til mig, saa vil jeg give eder det bedste, der er i Ægypten, og I skal nyde Landets Fedme.
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 Byd dem at gøre saaledes: Tag eder Vogne i Ægypten til eders Børn og Kvinder, sæt eders Fader op og kom hid;
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 bryd eder ikke om eders Ejendele, thi det bedste, der er i hele Ægypten, skal være eders!«
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 Det gjorde Israels Sønner saa. Og efter Faraos Bud gav Josef dem Vogne og Rejsekost med;
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 hver især gav han dem et Sæt Festklæder, men Benjamin gav han 300 Sekel Sølv og fem Sæt Festklæder;
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 og sin Fader sendte han ti Æsler med det bedste, der var i Ægypten og ti Aseninder med Korn, Brød og Rejsetæring til Faderen.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 Saa tog han Afsked med sine Brødre, og da de drog bort, sagde han til dem: »Kives ikke paa Vejen!«
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 Saaledes drog de hjem fra Ægypten og kom til deres Fader Jakob i Kana'ans Land;
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 og de fortalte ham det og sagde: »Josef lever endnu, og han er Hersker over hele Ægypten.« Men hans Hjerte blev koldt, thi han troede dem ikke.
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 Saa fortalte de ham alt, hvad Josef havde sagt til dem; og da han saa Vognene, som Josef havde sendt for at hente ham, oplivedes deres Fader Jakobs Aand atter;
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 og Israel sagde: »Det er stort, min Søn Josef lever endnu; jeg vil drage hen og se ham, inden jeg dør!«
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”