< 1 Mosebog 24 >
1 Abraham var blevet gammel og til Aars, og HERREN havde velsignet ham i alle Maader.
Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
2 Da sagde Abraham til sin Træl, sit Hus's ældste, som stod for hele hans Ejendom: »Læg din Haand under min Lænd,
Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
3 saa jeg kan tage dig i Ed ved HERREN, Himmelens og Jordens Gud, at du ikke vil tage min Søn en Hustru af Kana'anæernes Døtre, blandt hvem jeg bor,
Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
4 men drage til mit Land og min Hjemstavn og tage min Søn Isak en Hustru derfra!«
Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
5 Da sagde Trællen: »Men hvis nu Pigen ikke vil følge mig her til Landet, skal jeg saa bringe din Søn tilbage til det Land, du vandrede ud fra?«
Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
6 Abraham svarede: »Vogt dig vel for at bringe min Søn tilbage dertil!
Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
7 HERREN, Himmelens Gud, som tog mig bort fra min Faders Hus og min Hjemstavns Land, som talede til mig og tilsvor mig, at han vil give mit Afkom dette Land, han vil sende sin Engel foran dig, saa du kan tage min Søn en Hustru derfra;
Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
8 men hvis Pigen ikke vil følge dig, saa er du løst fra Eden til mig; men i intet Tilfælde maa du bringe min Søn tilbage dertil!«
In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
9 Da lagde Trællen sin Haand under sin Herre Abrahams Lænd og svor ham Eden.
Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
10 Derpaa tog Trællen ti af sin Herres Kameler og alle Haande kostbare Gaver fra sin Herre og gav sig paa Vej til Nakors By i Aram-Naharajim.
Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
11 Uden for Byen lod han Kamelerne knæle ved Brønden ved Aftenstid, ved den Tid Kvinderne gaar ud for at hente Vand;
Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
12 og han bad saaledes: »HERRE, du min Herre Abrahams Gud, lad det lykkes for mig i Dag og vis Miskundhed mod min Herre Abraham!
Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
13 Se, jeg stiller mig her ved Vandkilden, nu Bymændenes Døtre gaar ud for at hente Vand;
Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
14 og siger jeg nu til en Pige: Hæld din Krukke og giv mig at drikke! og siger saa hun: Drik kun, og jeg vil ogsaa give dine Kameler at drikke! lad det da være hende, du har udset til din Tjener Isak; saaledes vil jeg kunne kende, at du har vist Miskundhed mod min Herre!«
Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
15 Knap var han færdig med at bede, se, da kom Rebekka, en Datter af Betuel, der var en Søn af Abrahams Broder Nakors Hustru Milka, gaaende med Krukken paa Skulderen,
Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
16 en saare smuk Kvinde, Jomfru, endnu ikke kendt af nogen Mand. Hun steg ned til Kilden, fyldte sin Krukke og steg op igen.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
17 Da ilede Trællen hen til hende og sagde: »Giv mig lidt Vand at drikke af din Krukke!«
Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
18 Hun svarede: »Drik, Herre!« og løftede straks Krukken ned paa sin Haand og lod ham drikke;
Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
19 og da hun havde slukket hans Tørst, sagde hun: »Jeg vil ogsaa øse Vand til dine Kameler, til de har slukket deres Tørst.«
Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
20 Saa skyndte hun sig hen og tømte Krukken i Truget og løb tilbage til Brønden for at øse, og saaledes øste hun til alle hans Kameler.
Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
21 Imidlertid stod Manden og saa tavs paa hende for at faa at vide, om HERREN havde ladet hans Rejse lykkes eller ej;
Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
22 og da Kamelernes Tørst var slukket, tog han en gylden Næsering, der vejede en halv Sekel, og to Armbaand, der vejede ti Guldsekel, og satte dem paa hendes Arme;
Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
23 og han sagde til hende: »Sig mig, hvis Datter du er! Er der Plads til os i din Faders Hus for Natten?«
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
24 Hun svarede: »Jeg er Datter af Betuel, som Milka fødte Nakor; «
Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
25 og videre sagde hun: »Der er rigeligt baade af Straa og Foder hos os og Plads til at overnatte!«
Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
26 Da bøjede Manden sig og tilbad HERREN,
Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
27 idet han sagde: »Lovet være HERREN, min Herre Abrahams Gud, som ikke har unddraget min Herre sin Miskundhed og Trofasthed! HERREN har ført mig paa Vejen til min Herres Broders Hus.«
yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
28 Pigen løb imidlertid hjem og fortalte alt dette i sin Moders Hus.
Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
29 Men Rebekka havde en Broder ved Navn Laban; han løb ud til Manden ved Kilden;
Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
30 og da han saa Næseringen og Armbaandene paa sin Søsters Arme og hørte sin Søster Rebekka fortælle, hvad Manden havde sagt til hende, gik han ud til Manden, som stod med sine Kameler ved Kilden;
Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
31 og han sagde: »Kom, du HERRENS velsignede, hvorfor staar du herude? Jeg har ryddet op i Huset og gjort Plads til Kamelerne.«
Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
32 Saa kom Manden hen til Huset og tog Seletøjet af Kamelerne, og Laban bragte Straa og Foder til dem og Vand til Fodtvæt for Manden og hans Ledsagere.
Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
33 Men da der blev sat Mad for ham, sagde han: »Jeg vil intet nyde, før jeg har røgtet mit Ærinde!« De svarede: »Sig frem!«
Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
34 Saa sagde han: »Jeg er Abrahams Træl.
Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
35 HERREN har velsignet min Herre i rigt Maal, saa han er blevet en velstaaende Mand, og givet ham Smaakvæg og Hornkvæg, Sølv og Guld, Trælle og Trælkvinder, Kameler og Æsler;
Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
36 og Sara, min Herres Hustru, har født ham en Søn i hans Alderdom, og ham har han givet alt, hvad han ejer.
Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
37 Og nu har min Herre taget mig i Ed og sagt: Du maa ikke tage min Søn en Hustru blandt Kana'anæernes Døtre, i hvis Land jeg bor;
Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
38 Men du skal drage til min Faders Hus og min Slægt og tage min Søn en Hustru derfra!
amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
39 Og da jeg sagde til min Herre: Men hvis nu Pigen ikke vil følge med mig?
“Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
40 svarede han: HERREN, for hvis Aasyn jeg har vandret, vil sende sin Engel med dig og lade din Rejse lykkes, saa du kan tage min Søn en Hustru af min Slægt og min Faders Hus;
“Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
41 i modsat Fald er du løst fra Eden til mig; kommer du til min Slægt, og de ikke vil give dig hende, er du løst fra Eden til mig!
Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
42 Da jeg nu i Dag kom til Kilden, bad jeg saaledes: HERRE, du min Herre Abrahams Gud! Vilde du dog lade den Rejse lykkes, som jeg nu har for!
“Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
43 Se, jeg stiller mig her ved Kilden, og siger jeg nu til den Pige, der kommer for at øse Vand: Giv mig lidt Vand at drikke af din Krukke!
Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
44 og svarer saa hun: Drik selv, og jeg vil ogsaa øse Vand til dine Kameler! lad hende da være den Kvinde, HERREN har udset til min Herres Søn!
in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
45 Og knap var jeg færdig med at tale saaledes ved mig selv, se, da kom Rebekka med sin Krukke paa Skulderen og steg ned til Kilden og øste Vand, og da jeg sagde til hende: Giv mig noget at drikke!
“Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
46 løftede hun straks sin Krukke ned og sagde: Drik kun, og jeg vil ogsaa give dine Kameler at drikke! Saa drak jeg, og hun gav ogsaa Kamelerne at drikke.
“Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
47 Da spurgte jeg hende: Hvis Datter er du? Og hun sagde: Jeg er Datter af Betuel, Nakors og Milkas Søn! Saa satte jeg Ringen i hendes Næse og Armbaandene paa hendes Arme;
“Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
48 og jeg bøjede mig og tilbad HERREN, og jeg lovede HERREN, min Herre Abrahams Gud, som havde ført mig den rigtige Vej, saa jeg: kunde tage min Herres Broderdatter til hans Søn!
na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
49 Hvis I nu vil vise min Herre Godhed og Troskab, saa sig mig det, og hvis ikke, saa sig mig det, for at jeg kan have noget at rette mig efter!«
Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
50 Da sagde Laban og Betuel: »Denne Sag kommer fra HERREN, vi kan hverken gøre fra eller til!
Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
51 Der staar Rebekka foran dig, tag hende og drag bort, at hun kan: blive din Herres Søns Hustru, saaledes som HERREN har sagt!«
Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
52 Da Abrahams Træl hørte deres Ord, kastede han sig til Jorden for HERREN.
Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
53 Derpaa fremtog Trællen Sølv og Guldsmykker og Klæder og gav Rebekka dem, og til hendes Broder og Moder uddelte han Gaver.
Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
54 Saa spiste og drak han og hans Ledsagere og overnattede der. Da de var staaet op næste Morgen, sagde han: »Lad mig nu fare til min Herre!«
Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
55 Men Rebekkas Broder og Moder svarede: »Lad dog Pigen blive hos os i nogen Tid, en halv Snes Dage eller saa, siden kan du drage bort!«
Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
56 Da sagde han til dem: »Ophold mig ikke, nu HERREN har ladet min Rejse lykkes; lad mig fare! Jeg vil drage til min Herre!«
Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
57 De svarede; »Lad os kalde paa. Pigen og spørge hende selv!«
Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
58 Og de kaldte paa Rebekka og spurgte hende: »Vil du drage med denne Mand?« Hun svarede: »Ja, jeg vil!«
Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
59 Da tog de Afsked med deres, Søster Rebekka og hendes Amme og med Abrahams Træl og hans Ledsagere;
Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
60 og de velsignede Rebekka og sagde: »Maatte du, vor Søster, blive til ti Tusind Tusinder, og maatte dit Afkom indtage dine Fjenders Porte!«
Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
61 Saa brød Rebekka og hendes Piger op, og de satte sig paa Kamelerne og fulgte med Manden; og Trællen tog Rebekka og drog bort.
Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
62 Isak var imidlertid draget til Ørkenen ved Be'er-lahaj-ro'i, og han boede i Sydlandet.
Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
63 Da han engang ved Aftenstid var gaaet ud paa Marken for at bede, saa han op og fik Øje paa nogle Kameler, der nærmede sig.
Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
64 Men da Rebekka saa op og fik Øje paa Isak, lod hun sig glide ned af Kamelen
Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
65 og spurgte Trællen: »Hvem er den Mand der, som kommer os i Møde paa Marken?« Trællen svarede: »Det er min Herre!« Da tog hun sit Slør og tilhyllede sig.
ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
66 Men Trællen fortalte Isak alt, hvad han havde udrettet.
Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
67 Da førte Isak Rebekka ind i sin Moder Saras Telt og tog hende til Hustru; og han fik hende kær. Saaledes blev Isak trøstet efter sin Moder.
Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.