< 2 Mosebog 5 >
1 Derefter gik Moses og Aron hen og sagde til Farao: »Saa siger HERREN, Israels Gud: Lad mit Folk rejse, for at de kan holde Højtid for mig i Ørkenen!«
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 Men Farao sagde: »Hvem er HERREN, at jeg skulde adlyde ham og lade Israeliterne rejse? Jeg kender ikke noget til HERREN, og jeg vil heller ikke lade Israeliterne rejse!«
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 De svarede: »Hebræernes Gud har mødt os; tillad os nu at drage tre Dagsrejser ud i Ørkenen og ofre til HERREN vor Gud, for at han ikke skal slaa os med Pest eller Sværd!«
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 Men Ægypterkongen sagde til dem: »Hvorfor vil I, Moses og Aron, forstyrre Folket i dets Arbejde? Gaa til eders Trællearbejde!«
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 Og Farao sagde: »Folket er saa vist dovent nok; og nu vil I have dem fri fra deres Trællearbejde!«
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 Samme Dag udstedte Farao følgende Befaling til Fogederne over Folket og dets Opsynsmænd:
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 »I skal ikke mere som hidtil give Folket Halm til Teglarbejdet; de skal selv gaa ud og sanke Halm;
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 men alligevel skal I paalægge dem at lave lige saa mange Teglsten som hidtil, I maa ikke eftergive dem noget; thi de er dovne, og derfor er det, de raaber op og siger: Lad os drage ud og ofre til vor Gud!
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Strengt Arbejde skal de Mennesker have, for at de kan være optaget deraf og ikke af Løgnetale.«
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 Da gik Folkets Fogeder og Opsynsmænd ud og sagde til Folket: »Saaledes siger Farao: Jeg vil ikke mere give eder Halm;
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 gaa selv ud og sank eder Halm, hvor I kan finde det, men i eders Arbejde bliver der intet eftergivet!«
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 Da spredte Folket sig over hele Ægypten for at samle Halmstraa.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 Men Fogederne trængte paa og sagde: »I skal Dag for Dag yde fuldt Arbejde, ligesom dengang I fik Halm!«
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 Og Israeliternes Opsynsmænd, som Faraos Fogeder havde sat over dem, fik Prygl, og der blev sagt til dem: »Hvorfor stryger I ikke mere det fastsatte Antal Teglsten ligesom før?«
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 Da gik Israeliternes Opsynsmænd hen og raabte til Farao: »Hvorfor handler du saaledes med dine Trælle?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 Dine Trælle faar ingen Halm, og dog siger de til os: Lav Teglsten! Og dine Trælle faar Prygl; du forsynder dig mod dit Folk.«
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 Men han svarede: »I er dovne, det er det, I er! Derfor siger I: Lad os rejse ud og ofre til HERREN!
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Gaa nu hen og tag fat paa eders Arbejde; I faar ingen Halm, men I skal levere det samme Antal Teglsten!«
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 Israeliternes Opsynsmænd følte sig ilde stedt ved at skulle sige: »Der maa intet eftergives i, hvad I daglig skal skaffe af Teglsten!«
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 Og da de ved deres Bortgang fra Farao traf Moses og Aron, som stod og ventede paa dem,
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 sagde de til dem: »HERREN se til eder og dømme eder, fordi I har vakt Afsky mod os hos Farao og hans Tjenere og lagt dem et Sværd i Haanden til at dræbe os med!«
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 Da vendte Moses sig igen til HERREN og sagde: »Herre, hvorfor har du handlet ilde med dette Folk? Hvorfor har du udsendt mig?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 Siden jeg har været hos Farao og talt i dit Navn, har han handlet ilde med dette Folk, og frelst dit Folk har du ikke!«
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”