< 5 Mosebog 6 >
1 Dette er Budet, Anordningerne og Lovbudene, som HERREN eders Gud har paabudt at lære eder at handle efter i det Land, I skal over og tage i Besiddelse,
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
2 for at du alle dine Levedage maa frygte HERREN din Gud og holde alle hans Anordninger og Bud, som jeg giver dig, du selv, din Søn og din Sønnesøn, og faa et langt Liv.
saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
3 Hør derfor, Israel, og gør omhyggeligt efter dem, for at det kan gaa dig vel, og for at I maa blive overvættes talrige, saaledes som HERREN, dine Fædres Gud, har forjættet dig, i et Land, der flyder med Mælk og Honning.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
4 Hør, Israel! HERREN vor Gud, HERREN er een.
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
5 Og du skal elske HERREN din Gud af hele dit Hjerte, af hele din Sjæl og af hele din Styrke.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
6 Disse Bud, som jeg paalægger dig i Dag, skal du tage dig til Hjerte;
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
7 og du skal indprente dine Børn dem og tale om dem, baade naar du sidder i dit Hus, og naar du vandrer paa Vejen, baade naar du lægger dig, og naar du staar op;
Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
8 du skal binde dem som et Tegn om din Haand, de skal være som et Erindringsmærke paa din Pande,
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
9 og du skal skrive dem paa Dørstolperne af dit Hus og paa dine Porte.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
10 Og naar HERREN din Gud fører dig ind i det Land, han tilsvor dine Fædre Abraham, Isak og Jakob at ville give dig, store og smukke Byer, som du ikke har bygget,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
11 Huse, der er fulde af alt godt, som du ikke har samlet, udhuggede Cisterner, som du ikke har udhugget, Vingaarde og Olivenhaver, som du ikke har plantet, og du spiser dig mæt,
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
12 vogt dig da for at glemme HERREN, som førte dig ud af Ægypten, af Trællehuset;
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
13 HERREN din Gud skal du frygte, ham skal du dyrke, og ved hans Navn skal du sværge!
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
14 I maa ikke holde eder til andre Guder, til nogen af de omboende Folks Guder,
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
15 thi HERREN din Gud er en nidkær Gud i din Midte; ellers vil HERREN din Guds Vrede blusse op imod dig, saa han udrydder dig af Jorden.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
16 I maa ikke friste HERREN eders Gud, som I gjorde ved Massa.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
17 I skal omhyggeligt holde HERREN eders Guds Bud, Vidnesbyrd og Anordninger, som han har paalagt dig;
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
18 og du skal gøre, hvad der er ret og godt i HERRENS Øjne, for at det maa gaa dig vel, og du maa komme ind og faa det herlige Land i Eje, som HERREN tilsvor dine Fædre,
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
19 idet han jager alle dine Fjender bort foran dig, som HERREN har sagt!
Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
20 Naar din Søn i Fremtiden spørger dig: »Hvorledes har det sig med de Vidnesbyrd, Anordninger og Lovbud, som HERREN vor Gud gav eder?«
Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
21 saa skal du svare din Søn saaledes: »Vi var engang Faraos Trælle i Ægypten; men HERREN førte os ud af Ægypten med stærk Haand.
Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
22 Og HERREN udførte Tegn og store, ødelæggende Undere paa Ægypten, paa Farao og hele hans Hus, lige for vore Øjne;
A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
23 men os førte han ud derfra for at føre os ind og give os det Land, han havde tilsvoret vore Fædre.
Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
24 Dengang paalagde HERREN os at handle efter alle disse Anordninger, idet vi frygter HERREN vor Gud, for at det altid maa gaa os vel, for at han kan lade os blive i Live, som det hidtil er sket.
Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
25 Og vi skal staa som retfærdige for HERREN vor Guds Ansigt, naar vi handler efter alle disse Anordninger, saaledes som han har paalagt os!«
In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”