< Apostelenes gerninger 25 >

1 Da Festus nu havde tiltraadt sit Landshøvdingembede, drog han efter tre Dages Forløb fra Kæsarea op til Jerusalem.
Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima,
2 Da førte Ypperstepræsterne og de fornemste af Jøderne Klage hos ham imod Paulus og henvendte sig til ham,
inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus.
3 idet de med ondt i Sinde imod Paulus bade ham om at bevise dem den Gunst, at han vilde lade ham hente til Jerusalem; thi de lurede paa at slaa ham ihjel paa Vejen.
Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun’yan kwanto su kashe shi a hanya.
4 Da svarede Festus, at Paulus blev holdt bevogtet i Kæsarea, men at han selv snart vilde drage derned.
Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba.
5 „Lad altsaa,” sagde han, „dem iblandt eder, der have Myndighed dertil, drage med ned og anklage ham, dersom der er noget uskikkeligt ved Manden.”
Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”
6 Og da han havde opholdt sig hos dem ikke mere end otte eller ti Dage, drog han ned til Kæsarea, og den næste Dag satte han sig paa Dommersædet og befalede, at Paulus skulde føres frem.
Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa.
7 Men da han kom til Stede, stillede de Jøder, som vare komne ned fra Jerusalem, sig omkring ham og fremførte mange og svare Klagemaal, som de ikke kunde bevise,
Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.
8 efterdi Paulus forsvarede sig og sagde: „Hverken imod Jødernes Lov eller imod Helligdommen eller imod Kejseren har jeg syndet i noget Stykke.”
Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”
9 Men Festus, som vilde fortjene sig Tak af Jøderne, svarede Paulus og sagde: „Er du villig til at drage op til Jerusalem og der staa for min Domstol i denne Sag?”
Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”
10 Men Paulus sagde: „Jeg staar for Kejserens Domstol, og der bør jeg dømmes. Jøderne har jeg ingen Uret gjort, som ogsaa du ved helt vel.
Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai.
11 Dersom jeg saa har Uret og har gjort noget, som fortjener Døden, vægrer jeg mig ikke ved at dø; men hvis det, hvorfor disse anklage mig, intet har paa sig, da kan ingen prisgive mig til dem. Jeg skyder mig ind under Kejseren.”
In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”
12 Da talte Festus med sit Raad og svarede: „Du har skudt dig ind under Kejseren; du skal rejse til Kejseren.”
Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”
13 Men da nogle Dage vare forløbne, kom Kong Agrippa og Berenike til Kæsarea og hilste paa Festus.
Bayan’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma.
14 Og da de opholdt sig der i flere Dage, forelagde Festus Kongen Paulus's Sag og sagde: „Der er en Mand efterladt af Feliks som Fange;
Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure.
15 imod ham førte Jødernes Ypperstepræster og Ældste Klage, da jeg var i Jerusalem, og bade om Dom over ham.
Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.
16 Dem svarede jeg, at Romere ikke have for Skik at prisgive noget Menneske, førend den anklagede har Anklagerne personligt til Stede og faar Lejlighed til at forsvare sig imod Beskyldningen.
“Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu.
17 Da de altsaa kom sammen her, tøvede jeg ikke, men satte mig den næste Dag paa Dommersædet og bød, at Manden skulde føres frem.
Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin.
18 Men da Anklagerne stode omkring ham, fremførte de ingen saadan Beskyldning, som jeg havde formodet;
Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba.
19 men de havde nogle Stridsspørgsmaal med ham om deres egen Gudsdyrkelse og om en Jesus, som er død, men som Paulus paastod er i Live.
A maimako haka, sai suka kawo waɗansu’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai.
20 Men da jeg var tvivlraadig angaaende Undersøgelsen heraf, sagde jeg, om han vilde rejse til Jerusalem og der lade denne Sag paadømme.
Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi.
21 Men da Paulus gjorde Paastand paa at holdes bevogtet til Kejserens Kendelse, befalede jeg, at han skulde holdes bevogtet, indtil jeg kan sende ham til Kejseren.”
Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”
22 Da sagde Agrippa til Festus: „Jeg kunde ogsaa selv ønske at høre den Mand.” Men han sagde: „I Morgen skal du faa ham at høre.”
Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.” Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”
23 Næste Dag altsaa, da Agrippa og Berenike kom med stor Pragt og gik ind i Forhørssalen tillige med Krigsøversterne og Byens ypperste Mænd, blev paa Festus's Befaling Paulus ført frem.
Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus.
24 Og Festus siger: „Kong Agrippa, og alle I Mænd, som ere med os til Stede! her se I ham, om hvem hele Jødernes Mængde har henvendt sig til mig, baade i Jerusalem og her, raabende paa, at han ikke længer bør leve.
Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba.
25 Men jeg indsaa, at han intet havde gjort, som fortjente Døden, og da han selv skød sig ind under Kejseren, besluttede jeg at sende ham derhen.
Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma.
26 Dog har jeg intet sikkert at skrive om ham til min Herre. Derfor lod jeg ham føre frem for eder og især for dig, Kong Agrippa! for at jeg kan have noget at skrive, naar Undersøgelsen er sket.
Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta.
27 Thi det synes mig urimeligt at sende en Fange uden ogsaa at angive Beskyldningerne imod ham.”
Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”

< Apostelenes gerninger 25 >