< 2 Samuel 20 >
1 Nu var der tilfældigvis en slet Person ved Navn Sjeba, Bikris Søn, en Benjaminit. Han stødte i Hornet og sagde: »Vi har ingen Del i David, ingen Lod i Isajs Søn! Hver Mand til sine Telte, Israel!«
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 Da faldt alle Israels Mænd fra David og gik over til Sjeba, Bikris Søn, medens Judas Mænd trofast fulgte deres Konge fra Jordan til Jerusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 Da David kom til sit Hus i Jerusalem, tog Kongen sine ti Medhustruer, som han havde ladet tilbage for at se efter Huset, og lod dem bringe til et bevogtet Hus, hvor han sørgede for deres Underhold; men han gik ikke mere ind til dem, og saaledes levede de indespærret til deres Dødedag som Kvinder, der er Enker, skønt deres Mænd endnu lever.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Derpaa sagde Kongen til Amasa: »Stævn Judas Mænd sammen i Løbet af tre Dage og indfind dig da her!«
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 Amasa gik saa bort for at stævne Judas Mænd sammen. Men da han tøvede ud over den fastsatte Frist,
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 sagde David til Abisjaj: »Nu bliver Sjeba, Bikris Søn, os farligere end Absalom! Tag derfor din Herres Folk og sæt efter ham, for at han ikke skal kaste sig ind i befæstede Byer og slippe fra os!«
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 Med Abisjaj drog Joab, Kreterne og Pleterne og alle Kærnetropperne ud fra Jerusalem for at sætte efter Sjeba, Bikris Søn.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 Men da de var ved den store Sten i Gibeon, kom Amasa dem i Møde. Joab var iført sin Vaabenkjortel, og over den havde han spændt et Sværd, hvis Skede var bundet til hans Lænd; og det gled ud og faldt til Jorden.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Joab sagde da til Amasa: »Gaar det dig vel, Broder?« Og Joab greb med højre Haand om Amasas Skæg for at kysse ham.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 Men Amasa tog sig ikke i Vare for det Sværd, Joab havde i sin venstre Haand; Joab stødte det i Underlivet paa ham, saa hans Indvolde væltede ud paa Jorden, og han døde ved det ene Stød. Derpaa satte Joab og hans Broder Abisjaj efter Sjeba, Bikris Søn,
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 medens en af Joabs Folk blev staaende ved Amasa og raabte: »Enhver, der bryder sig om Joab og holder med David, følge efter Joab!«
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 Men Amasa laa midt paa Vejen, svømmende i sit Blod, og da Manden saa, at alt Folket stod stille der, væltede han Amasa fra Vejen ind paa Marken og kastede en Kappe over ham; thi han saa, at alle, der kom forbi, stod stille.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 Saa snart han var fjernet fra Vejen, fulgte alle efter Joab for at sætte efter Sjeba, Bikris Søn.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Denne drog imidlertid gennem alle Israels Stammer indtil Abel-Bet-Ma'aka, og alle Bikriterne samlede sig og fulgte ham.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 Da kom de og belejrede ham i Abel-Bet-Ma'aka, idet de opkastede en Vold om Byen. Men medens alt Krigsfolket, der var med Joab, arbejdede paa at bringe Muren til Fald,
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 traadte en klog Kvinde fra Byen hen paa Formuren og raabte: »Hør, hør! Sig til Joab, at han skal komme herhen; jeg vil tale med ham!«
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 Da han kom hen til hende, spurgte Kvinden: »Er du Joab?« Og da han svarede ja, sagde hun: »Hør din Trælkvindes Ord!« Han svarede: »Jeg hører!«
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 Saa sagde hun: »I gamle Dage sagde man: Man spørge dog i Abel og Dan, om det er gaaet af Brug, hvad gode Folk i Israel vedtog!
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 Og nu søger du at bringe Død over en By, som er en Moder i Israel! Hvorfor vil du ødelægge HERRENS Arvelod?«
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 Joab svarede: »Det være langt fra mig, det være langt fra mig at ødelægge eller volde Fordærv!
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 Saaledes er det ingenlunde ment! Men en Mand fra Efraims Bjerge ved Navn Sjeba, Bikris Søn, har løftet sin Haand mod Kong David; hvis I blot vil udlevere ham, bryder jeg op fra Byen!« Da sagde Kvinden til Joab: »Hans Hoved skal blive kastet ned til dig gennem Muren!«
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Kvinden fik saa ved sin Klogskab hele Byen overtalt til at hugge Hovedet af Sjeba, Bikris Søn, og de kastede det ned til Joab. Da stødte han i Hornet, og de brød op fra Byen og spredte sig hver til sit, medens Joab selv vendte tilbage til Kongen i Jerusalem.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Joab stod over hele Israels Hær; Benaja, Jojadas Søn, over Kreterne og Pleterne;
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 Adoniram havde Tilsynet med Hoveriarbejdet; Josjafat, Ahiluds Søn, var Kansler;
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 Sjeja var Statsskriver, Zadok og Ebjatar Præster;
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 ogsaa Ja'iriten Ira var Præst hos David.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.