< Anden Kongebog 13 >

1 I Ahazjas Søns, Kong Joas af Judas, tre og tyvende Regeringsaar blev Joahaz, Jehus Søn, Konge over Israel, og han herskede sytten Aar i Samaria.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, og vandrede i de Synder, Jeroboam, Nebats Søn, havde forledt Israel til; fra dem veg han ikke.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 Da blussede HERRENS Vrede op mod Israel, og han gav dem til Stadighed i Kong Hazael af Arams og hans Søn Benhadads Haand.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Men Joahaz bad HERREN om Naade, og HERREN bønhørte ham, fordi han saa Israels Trængsel; thi Arams Konge bragte Trængsel over dem;
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 og HERREN gav Israel en Befrier, som friede dem af Arams Haand; saa boede Israeliterne i deres Telte som før.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Dog veg de ikke fra de Synder, Jeroboams Hus havde forledt Israel til, men vandrede i dem; ogsaa Asjerastøtten blev staaende i Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Thi Arams Konge levnede ikke Joahaz flere Krigsfolk end halvtredsindstyve Ryttere, ti Stridsvogne og ti Tusinde Mand Fodfolk, men han tilintetgjorde dem og knuste dem til Støv.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Hvad der ellers er at fortælle om Joahaz, alt, hvad han udførte, og hans Heltegerninger staar jo optegnet i Israels Kongers Krønike.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 Saa lagde Joahaz sig til Hvile hos sine Fædre, og man jordede ham i Samaria; og hans Søn Joas blev Konge i hans Sted.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 I Kong Joas af Judas syv og tredivte Regeringsaar blev Joas, Joahaz's Søn, Konge over Israel, og han herskede seksten Aar i Samaria.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, og veg ikke fra nogen af de Synder, Jeroboam, Nebats Søn, havde forledt Israel til, men vandrede i dem.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 Hvad der ellers er at fortælle om Joas, alt, hvad han udførte, og hans Heltegerninger, hvorledes han førte Krig med Kong Amazja af Juda, staar jo optegnet i Israels Kongers Krønike.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 Saa lagde Joas sig til Hvile hos sine Fædre; og Jeroboam satte sig paa hans Trone. Joas blev jordet i Samaria hos Israels Konger.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Da Elisa blev ramt af den Sygdom, han døde af, kom Kong Joas af Israel ned til ham, bøjede sig grædende over ham og sagde: »Min Fader, min Fader, du Israels Vogne og Ryttere!«
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Men Elisa sagde til ham: »Bring Bue og Pile!« Og han bragte ham Bue og Pile.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Da sagde han til Israels Konge: »Læg din Haand paa Buen!« Og da han gjorde det, lagde Elisa sine Hænder paa Kongens
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 og sagde: »Luk Vinduet op mod Øst!« Og da han havde gjort det, sagde Elisa: »Skyd!« Og han skød. Da sagde Elisa: »En Sejrspil fra HERREN, en Sejrspil mod Aram! Du skal tilføje Aram et afgørende Nederlag ved Afek!«
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Derpaa sagde han: »Tag Pilene!« Og han tog dem. Da sagde han til Israels Konge: »Slaa paa Jorden!« Og han slog tre Gange, men holdt saa op.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Da vrededes den Guds Mand paa ham og sagde: »Du burde have slaaet fem-seks Gange, saa skulde du have tilføjet Aram et afgørende Nederlag, men nu skal du kun slaa Aram tre Gange!«
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Saa døde Elisa, og de jordede ham. Aar efter Aar trængte moabitiske Strejfskarer ind i Landet;
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 og da nogle Israeliter engang fik Øje paa en saadan Skare, netop som de var ved at jorde en Mand, kastede de Manden i Elisas Grav og løb deres Vej. Men da Manden kom i Berøring med Elisas Ben, blev han levende og rejste sig op.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Kong Hazael af Aram trængte Israel haardt, saa længe Joahaz levede.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 Men HERREN forbarmede sig og ynkedes over dem og vendte sig til dem paa Grund af sin Pagt med Abraham, Isak og Jakob; han vilde ikke tilintetgøre dem og havde endnu ikke stødt dem bort fra sit Aasyn.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Men da Kong Hazael af Aram døde, og hans Søn Benhadad blev Konge i hans Sted,
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 tog Joas, Joahaz's Søn, de Byer tilbage fra Benhadad, Hazaels Søn, som han i Krigen havde frataget hans Fader Joahaz. Tre Gange slog Joas ham og tog de israelitiske Byer tilbage.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< Anden Kongebog 13 >