< Anden Kongebog 10 >

1 Der var i Samaria halvfjerdsindstyve Sønner af Akab. Jehu skrev nu Breve og sendte dem til Samaria til Byens Øverster, de Ældste og Akabs Sønners Fosterfædre. Deri stod:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 »I har jo eders Herres Sønner hos eder og raader over Stridsvognene og Hestene, Fæstningerne og Vaabenforraadene. Naar nu dette Brev kommer eder i Hænde,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 udvælg saa den bedste og dygtigste af eders Herres Sønner, sæt ham paa hans Faders Trone og kæmp for eders Herres Hus!«
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 Men de grebes af stor Forfærdelse og sagde: »Se, de to Konger kunde ikke staa sig imod ham, hvor skal vi saa kunne det?«
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 Derfor sendte Paladsets og Byens øverste Befalingsmænd, de Ældste og Fosterfædrene det Bud til Jehu: »Vi er dine Trælle, og alt, hvad du kræver af os, vil vi gøre. Vi vil ikke gøre nogen til Konge; gør, hvad du finder for godt!«
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Da skrev han et nyt Brev til dem, og der stod: »Dersom I holder med mig og vil høre mig, tag saa eders Herres Sønners Hoveder og kom i Morgen ved denne Tid til mig i Jizre'el!« Kongesønnerne, halvfjerdsindstyve Mænd, var nemlig hos Byens Stormænd, som var deres Fosterfædre.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 Da Brevet kom til dem, tog de Kongesønnerne og dræbte dem, halvfjerdsindstyve Mænd, lagde deres Hoveder i Kurve og sendte dem til Jehu i Jizre'el.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Da Budet kom og meldte: »Kongesønnernes Hoveder er bragt hid!« sagde han: »Læg dem i to Bunker foran Porten til i Morgen!«
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 Næste Morgen gik han ud, traadte frem og sagde til alt Folket: »I er uden Skyld; det er mig, der har stiftet en Sammensværgelse mod min Herre og dræbt ham — men hvem har dræbt alle disse?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Kend nu, at intet af det Ord, HERREN talede mod Akabs Hus, var faldet til Jorden, men HERREN har gjort, hvad han talede ved sin Tjener Elias!«
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 Derpaa lod Jehu alle dem, der var tilbage af Akabs Hus i Jizre'el, dræbe, alle hans Stormænd, Venner og Præster, saa at ikke en eneste blev tilbage og slap bort.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 Saa brød han op og drog ad Samaria til. Da han kom til Bet-Eked-Haro'im ved Vejen,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 mødte han Kong Ahazja af Judas Brødre. Han spurgte dem: »Hvem er I?« De svarede: »Vi er Ahazjas Brødre, og vi drager herned for at hilse paa Kongens og Kongemoderens Sønner.«
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 Da sagde han: »Grib dem levende!« Saa greb de dem levende, og han lod dem dræbe ved Bet-Ekeds Brønd, to og fyrretyve Mænd; ikke een lod han blive tilbage.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 Da han drog videre, traf han Jonadab, Rekabs Søn, der kom ham i Møde, og han hilste paa ham og spurgte: »Er du af Hjertet oprigtig mod mig som jeg mod dig?« Jonadab svarede: »Ja, jeg er!« Da sagde Jehu: »Saa giv mig din Haand!« Han gav ham da Haanden, og Jehu tog ham op til sig i Vognen
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 og sagde: »Følg mig og se min Nidkærhed for HERREN!« Og han tog ham med i Vognen,
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 Saa drog han til Samaria og lod alle, der var tilbage af Akabs Slægt i Samaria, dræbe, saa at den blev fuldstændig udryddet efter det Ord, HERREN havde talet til Elias.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Derefter kaldte Jehu hele Folket sammen og sagde til dem: »Akab dyrkede Ba'al lidt, Jehu vil dyrke ham mere!
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Kald derfor alle Ba'als Profeter, alle, der dyrker ham, og alle hans Præster hid til mig, ikke een maa udeblive, thi jeg har et stort Slagtoffer for til Ære for Ba'al; enhver, der udebliver, skal bøde med Livet!« Men det var en Fælde, Jehu stillede, for at udrydde Ba'alsdyrkerne.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 Derpaa sagde Jehu: »Helliger en festlig Samling til Ære for Ba'al!« Og de udraabte en festlig Samling.
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 Og Jehu sendte Bud rundt i hele Israel, og alle Ba'alsdyrkerne uden Undtagelse indfandt sig; de begav sig til Ba'als Hus, og det blev fuldt fra Ende til anden.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Saa sagde han til Opsynsmanden over Klædekammeret: »Tag en Klædning frem til hver af Ba'alsdyrkerne!« Og han tog Klædningerne frem til dem.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 Saa gik Jehu og Jonadab, Rekabs Søn, ind i Ba'als Hus; og han sagde til Ba'alsdyrkerne: »Se nu godt efter; at der ikke her iblandt eder findes nogen, som dyrker HERREN, men kun Ba'alsdyrkere!«
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 Derpaa gik han ind for at ofre Slagtofre og Brændofre. Men Jehu havde opstillet firsindstyve Mand udenfor og sagt: »Den, der lader nogen af de Mænd undslippe, som jeg overgiver i eders Hænder, skal bøde Liv for Liv!«
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 Da han saa var færdig med at ofre Brændofferet, sagde han til Livvagten og Høvedsmændene: »Gaa nu ind og hug dem ned! Ikke een maa slippe bort!« Og de huggede dem ned med Sværdet, og Livvagten og Høvedsmændene slængte dem bort; saa gik de ind i Ba'alshusets inderste Rum,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 bragte Ba'alshusets Asjerastøtte ud og opbrændte den;
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 og de nedbrød Ba'als Stenstøtte, rev Ba'als Hus ned og gjorde det til Nødtørftssteder, og de er der den Dag i Dag.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 Saaledes udryddede Jehu Ba'al af Israel.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Men fra de Synder, Jeroboam, Nebats Søn, havde forledt Israel til, Guldkalvene i Betel og Dan, veg Jehu ikke.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 Og HERREN sagde til Jehu: »Fordi du har handlet vel og gjort, hvad der er ret i mine Øjne, og handlet med Akabs Hus ganske efter mit Sind, skal dine Sønner sidde paa Israels Trone indtil fjerde Led!«
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 Men Jehu tog ikke Vare paa at følge HERRENS, Israels Guds, Lov af hele sit Hjerte; han veg ikke fra de Synder, Jeroboam havde forledt Israel til.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 Paa den Tid begyndte HERREN at rive Stykker fra Israel, og Hazael slog Israel i alle dets Grænseegne,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 Øst for Jordan, hele Gilead, Gaditernes, Rubeniternes og Manassiternes Land fra Aroer ved Arnonflodens Bred, baade Gilead og Basan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Hvad der ellers er at fortælle om Jehu, alt, hvad han gjorde, og alle hans Heltegerninger, staar jo optegnet i Israels Kongers Krønike.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 Saa lagde Jehu sig til Hvile hos sine Fædre, og man jordede ham i Samaria; og hans Søn Joahaz blev Konge i hans Sted.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Den Tid, Jehu herskede over Israel, udgjorde otte og tyve Aar.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< Anden Kongebog 10 >