< Anden Krønikebog 31 >
1 Da alt det var til ende, drog alle de Israeliter, som var til stede, ud til Judas Byer, og de sønderbrød Stenstøtterne, omhuggede Asjerastøtterne og nedrev Offerhøjene og Altrene i hele Juda og Benjamin og i Efraim og Manasse, saa der ikke blev Spor tilbage; saa vendte alle Israeliterne hjem, hver til sin Ejendom i deres Byer.
Sa’ad da aka gama dukan wannan, sai Isra’ilawan da suke can suka fita zuwa garuruwan Yahuda, suka rurrushe keɓaɓɓun duwatsu suka kuma farfashe ginshiƙan Ashera. Suka rurrushe masujadan kan tudu da bagadai, ko’ina a Yahuda da Benyamin da kuma cikin Efraim da Manasse. Bayan sun rurrushe dukansu, sai Isra’ilawa suka koma garuruwansu, kowanne zuwa mahallinsa.
2 Saa ordnede Ezekias Præsternes og Leviternes Skifter, Skifte for Skifte, saa at hver enkelt Præst og Levit fik sin særlige Gerning med at ofre Brændofre og Takofre og med af gøre Tjeneste og love og prise i HERRENS Lejrs Porte.
Hezekiya kuma ya raba firistoci da Lawiyawa kashi-kashi, kowanne da hidimarsa, firistoci da Lawiyawa, don hadayu na ƙonawa da na salama, su yi hidima, su yi godiya, su kuma rera yabai a ƙofofin mazaunin Ubangiji.
3 Hvad Kongen gav af sit Gods, var til Brændofrene, Morgen— og Aftenbrændofrene og Brændofrene paa Sabbaterne, Nymaanerne og Højtiderne, som det er foreskrevet i HERRENS Lov.
Sarki ya ba da taimako daga mallakarsa domin hadayun ƙonawa, safe da yamma da kuma don hadayun ƙonawa a Asabbatai, Sabon Wata da kuma ƙayyadaddun bukukkuwa kamar yadda yake a rubuce a cikin Dokar Ubangiji.
4 Og han bød Folket, dem, der boede i Jerusalem, at afgive, hvad der tilkom Præsterne og Leviterne, for at de kunde holde fast ved HERRENS Lov.
Ya umarci mutanen da suke zama a Urushalima su ba da rabon da yake na firistoci da Lawiyawa, don su ƙwallafa ransu ga Dokar Ubangiji.
5 Saa snart det Bud kom ud, bragte Israeliterne i rigelig Mængde Førstegrøde af Korn, Most, Olie og Honning og al Markens Afgrøde, og de gav Tiende af alt i rigeligt Maal;
Nan da nan aka baza umarnin, sai Isra’ilawa suka bayar’ya’yan farin hatsinsu, sabon ruwan inabi, mai da kuma zuma da dukan abin da gona ta bayar, hannu sake. Suka kawo zakan kowane abu da yawa.
6 ogsaa de Israeliter, der boede i Judas Byer, gav Tiende af Hornkvæg og Smaakvæg, og de bragte Helliggaverne, der var helliget HERREN deres Gud, og lagde dem Bunke for Bunke.
Mutanen Isra’ila da Yahuda waɗanda suke zama a garuruwan Yahuda, su ma suka kawo zakan shanu da na tumaki da kuma zakan abubuwa masu tsarki da aka keɓe ga Ubangiji Allahnsu, suka jibge su tsibi-tsibi.
7 I den tredje Maaned begyndte de at ophobe Bunkerne, og i den syvende Maaned var de færdige.
Sun fara yin haka a wata na uku, suka kuma gama a wata na bakwai.
8 Ezekias og Øversterne kom saa og synede Bunkerne, og de priste HERREN og hans Folk Israel.
Sa’ad da Hezekiya da fadawansa suka zo suka ga tsibin, sai suka yabi Ubangiji, suka kuma albarkace mutanensa Isra’ila.
9 Da Ezekias spurgte sig for hos Præsterne og Leviterne om Bunkerne,
Hezekiya ya tambayi firistoci da Lawiyawa game da tsibin;
10 svarede Ypperstepræsten Azarja af Zadoks Hus: »Siden man begyndte at bringe Offerydelsen til HERRENS Hus, har vi spist os mætte og faaet rigelig tilovers, thi HERREN har velsignet sit Folk, saa at vi har faaet al den Rigdom her tilovers!«
sai Azariya babban firist, daga iyalin Zadok ya amsa, “Tun daga lokacin da mutane suka fara kawo taimakonsu ga haikalin Ubangiji, muna da isashe don abinci da kuma da yawa da za mu rage, domin Ubangiji ya albarkaci mutanensa, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”
11 Ezekias gav da Befaling til at indrette Kamre i HERRENS Hus; og det gjorde man.
Hezekiya ya ba da umarni a shirya ɗakunan ajiya a haikalin Ubangiji, aka kuwa yi haka.
12 Saa bragte man samvittighedsfuldt Offerydelsen, Tienden og Helliggaverne derind. Den øverste Opsynsmand derover var Leviten Konanja, den næstøverste hans Broder Sjim'i;
Sa’an nan cikin aminci suka kawo taimako, zakka da keɓaɓɓun kyautai. Konaniya, wani Balawe, shi ne ke lura da waɗannan abubuwa, kuma ɗan’uwansa Shimeyi shi ne na biye da shi.
13 og Jehiel, Azarja, Nahat, Asa'el, Jerimot, Jozabad, Eliel, Jismakjahu, Mahat og Benaja var Opsynsmænd under Konanja og hans Broder Sjim'i efter den Ordning, som var truffet af Ezekias og Azarja, Øversten i Guds Hus.
Yehiyel, Azaziya, Nahat, Asahel, Yerimot, Yozabad, Eliyel, Ismakiya, Mahat da Benahiya su ne shugabanni, mataimakan Konaniya da Shimeyi ɗan’uwansa, waɗanda sarki Hezekiya da Azariya babban shugaban haikalin Allah suka naɗa.
14 Leviten Kore, Jimnas Søn, der var Dørvogter paa Østsiden, havde Tilsyn med de frivillige Gaver til Gud og skulde uddele HERRENS Offerydelse og de højhellige Gaver;
Kore ɗan Imna Balawe, mai tsaron Ƙofar Gabas, shi ne yake lura da baikon yardan ran da aka yi wa Allah, don ya karkasa bayarwar da aka keɓe domin Ubangiji da hadayu mafi tsarki.
15 under ham sattes Eden, Minjamin, Jesua, Sjemaja, Amarja og Sjekanja i Præstebyerne til samvittighedsfuldt at forestaa Uddelingen til deres Brødre i Skifterne, baade store og smaa,
Eden, Miniyamin, Yeshuwa, Shemahiya, Amariya da Shekaniya sun taimake shi da aminci a cikin garuruwan firistoci, suna ba da rabo wa’yan’uwansu firistoci bisa ga sassansu, tsofaffi da yara.
16 dem af Mandkøn, der var indført i Fortegnelserne fra Treaarsalderen og opefter. Undtaget var alle, der kom til HERRENS Hus for efter de enkelte Dages Krav at udføre deres Embedsgerning efter deres Skifter.
Bugu da ƙari, suka ba da rabo ga maza’yan shekaru uku ko fiye waɗanda sunayensu suna a tarihin zuriya, dukan waɗanda ba za su iya shiga haikalin Ubangiji su yi ayyukansu na kullum ba, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
17 Præsterne indførtes i Fortegnelserne efter deres Fædrenehuse, Leviterne fra Tyveaarsalderen og opefter efter deres Embedspligter, efter deres Skifter,
Suka kuma ba da rabo ga firistocin da aka rubuta ta iyalansu cikin tarihin zuriya, haka kuma ga Lawiyawa masu shekara ashirin ko fiye, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
18 Og de indførtes i Fortegnelserne med hele deres Familie, deres Hustruer, Sønner og Døtre, hele Standen, thi de tog sig samvittighedsfuldt af det hellige.
Suka haɗa da dukan ƙanana’ya’yansu, mata, da kuma’ya’ya maza da’ya’ya mata, al’umma gaba ɗaya da aka jera a waɗannan tarihin zuriya. Gama sun yi aminci cikin tsarkake kansu.
19 Arons Sønner, Præsterne, som boede paa Græsmarkerne omkring deres Byer, havde i hver By nogle navngivne Mænd til at uddele, hvad der tilkom alle af Mandkøn blandt Præsterne og de i Fortegnelserne indførte Leviter.
Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa’ya’yan Haruna, firist, maza, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namijin da aka rubuta na Lawiyawa, rabonsa.
20 Saaledes gik Ezekias frem i hele Juda, og han gjorde, hvad der var godt, ret og sandt for HERREN hans Guds Aasyn.
Abin da Hezekiya ya yi ke nan ko’ina a Yahuda, yana yin abin da yake da kyau, daidai da kuma mai aminci a gaban Ubangiji Allahnsa.
21 Alt, hvad han tog fat paa vedrørende Tjenesten i Guds Hus eller Loven eller Budet for saaledes at søge sin Gud, det gjorde han af hele sit Hjerte, og det lykkedes for ham.
Cikin kome da ya yi cikin hidimar haikalin Allah, cikin biyayya kuma ga doka da umarnai, ya nemi Allahnsa, ya kuma yi aiki gabagadi. Ta haka kuwa ya yi nasara.