< Anden Krønikebog 22 >
1 Derpaa gjorde Jerusalems Indbyggere hans yngste Søn Ahazja til Konge i hans Sted, thi de ældre var dræbt af Røverskaren, der brød ind i Lejren sammen med Araberne. Saaledes blev Ahazja, Jorams Søn, Konge i Juda.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Ahazja var to og fyrretyve Aar gammel, da han blev Konge, og han herskede eet Aar i Jerusalem. Hans Moder hed Atalja og var Datter af Omri.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 Ogsaa han vandrede i Akabs Hus's Spor, thi hans Moder forledte ham til Ugudelighed ved sine Raad.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, ligesom Akabs Hus, thi efter Faderens Død blev de hans Raadgivere, og det blev hans Fordærv.
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 Det var ogsaa efter deres Raad, han sammen med Akabs Søn, Kong Joram af Israel, drog i Krig mod Kong Hazael af Aram ved Ramot i Gilead. Men Aramæerne saarede Joram.
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 Saa vendte Joram tilbage for i Jizre'el at søge Helbredelse for de Saar, man havde tilføjet ham ved Rama, da han kæmpede med Kong Hazael af Aram; og Jorams Søn, Kong Ahazja af Juda, drog ned for at se til Joram, Akabs Søn, i Jizre'el, fordi han laa syg.
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 Men til Ahazjas Undergang var det tilskikket af Gud, at han skulde komme til Joram; thi da han var kommet derhen, gik han med Joram ud til Jehu, Nimsjis Søn, som HERREN havde salvet til at udrydde Akabs Hus.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 Og da Jehu fuldbyrdede Dommen over Akabs Hus, traf han paa Judas Øverster og Ahazjas Brodersønner, der var i Ahazjas Tjeneste, og dræbte dem;
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 derpaa lod han Ahazja eftersøge, og man fangede ham, medens han holdt sig skjult i Samaria, og bragte ham til Jehu, der lod ham dræbe. Saa jordede de ham, thi de sagde: »Han var dog en Søn af Josafat, der søgte HERREN af hele sit Hjerte.« Men af Ahazjas Hus var ingen stærk nok til at tage Magten.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 Da Atalja, Ahazjas Moder, fik at vide, at hendes Søn var død, tog hun sig for at udrydde hele den kongelige Slægt af Judas Hus.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 Men Kongens Datter Josjab'at tog Ahazjas Søn Joas og fik ham hemmeligt af Vejen, saa han ikke var imellem Kongesønnerne, der blev dræbt, og hun gemte ham og hans Amme i Sengekammeret. Saaledes holdt Josjab'at, Kong Jorams Datter, Præsten Jojadas Hustru, der jo var Søster til Ahazja, ham skjult for Atalja, saa hun ikke fik ham dræbt;
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 og han var i seks Aar skjult hos dem i HERRENS Hus, medens Atalja herskede i Landet.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.