< 1 Samuel 5 >

1 Filisterne tog da Guds Ark og bragte den fra Eben Ezer til Asdod.
Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
2 Og Filisterne tog Guds Ark og bragte den ind i Dagons Hus og stillede den ved Siden af Dagon.
Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
3 Men tidligt næste Morgen, da Asdoditerne gik ind i Dagons Hus, se, da var Dagon faldet næsegrus til Jorden foran HERRENS Ark. De tog da Dagon og stillede ham paa Plads igen.
Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
4 Men da de kom tidligt næste Morgen, se, da var Dagon faldet næsegrus til Jorden foran HERRENS Ark; Hovedet og begge Hænder var slaaet af og laa paa Tærskelen; kun Kroppen var tilbage af ham.
Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
5 Derfor undgaar Dagons Præster og alle, som gaar ind i Dagons Hus, endnu den Dag i Dag at træde paa Dagons Tærskel i Asdod.
Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
6 Og HERRENS Haand laa tungt paa Asdoditerne; han bragte Fordærvelse over dem, og med Pestbylder slog han Asdod og Egnen der omkring.
Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
7 Da Asdoditerne skønnede, hvorledes det hang sammen, sagde de: »Israels Guds Ark maa ikke blive hos os, thi hans Haand tager haardt paa os og paa Dagon, vor Gud!«
Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
8 De sendte da Bud og kaldte alle Filisterfyrsterne sammen hos sig og sagde: »Hvad skal vi gøre med Israels Guds Ark?« De svarede: »Israels Guds Ark skal flyttes til Gat!« Saa flyttede de Israels Guds Ark;
Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
9 men efter at de havde flyttet den derhen, ramte HERRENS Haand Byen, saa de grebes af stor Rædsel; og han slog Indbyggerne i Byen, smaa og store, saa der brød Pestbylder ud paa dem.
Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
10 De sendte da Guds Ark til Ekron; men da Guds Ark kom til Ekron, raabte Ekroniterne: »De har flyttet Israels Guds Ark over til mig for at bringe Død over mig og mit Folk!«
Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
11 Og de sendte Bud og kaldte alle Filisterfyrsterne sammen og sagde: »Send Israels Guds Ark bort og lad den komme hen igen, hvor den har hjemme, for at den ikke skal bringe Død over mig og mit Folk!« Thi der var kommet Dødsangst over hele Byen, Guds Haand laa saare tungt paa den.
Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
12 De Mænd, som ikke døde, blev slaaet med Pestbylder, saa at Klageraabet fra Byen naaede op til Himmelen.
Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.

< 1 Samuel 5 >