< 1 Samuel 10 >

1 Da tog Samuel Olieflasken og udgød Olien over hans Hoved, kyssede ham og sagde: »Har HERREN ikke salvet dig til Fyrste over sit Folk Israel? Du skal herske over HERRENS Folk og frelse det fra dets Fjender. Og dette skal være dig Tegnet paa, at HERREN har salvet dig til Fyrste over sin Arv:
Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
2 Naar du i Dag gaar fra mig, skal du træffe to Mænd ved Rakels Grav ved Benjamins Grænse i Zelza, og de skal sige til dig: Æslerne, du gik ud at lede efter, er fundet; dem har din Fader slaaet af Tanke, men nu er han urolig for eder og siger: Hvad skal jeg gøre for min Søn?
Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
3 Og naar du er gaaet et Stykke længere frem og kommer til Taboregen, skal du træffe tre Mænd, som er paa Vej op til Gud i Betel; den ene bærer tre Kid, den anden tre Brødkager og den tredje en Dunk Vin;
“Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
4 de skal hilse paa dig og give dig to Brødkager, som du skal tage imod.
Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
5 Derefter kommer du til Guds Gibea, hvor Filisternes Foged bor; og naar du kommer hen til Byen, vil du støde paa en Flok Profeter, som kommer ned fra Offerhøjen i profetisk Henrykkelse til Harpers, Paukers, Fløjters og Citres Klang;
“Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
6 saa vil HERRENS Aand overvælde dig, saa du falder i profetisk Henrykkelse sammen med dem, og du skal blive til et andet Menneske.
Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
7 Naar disse Tegn indtræffer for dig, kan du trygt gøre, hvad der falder for; thi Gud er med dig.
Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
8 Og du skal gaa i Forvejen ned til Gilgal; saa kommer jeg ned til dig for at bringe Brændofre og ofre Takofre. Syv Dage skal du vente, til jeg kommer og kundgør dig, hvad du skal gøre!«
“Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
9 Da han derpaa vendte sig for at gaa bort fra Samuel, gav Gud ham et helt andet Hjerte, og alle disse Tegn indtraf samme Dag.
Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
10 Da han kom hen til Gibea, se, da kom en Flok Profeter ham i Møde, og Guds Aand overvældede ham, og han faldt i profetisk Henrykkelse midt iblandt dem.
Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
11 Og da alle, som kendte ham fra tidligere Tid, saa ham i profetisk Henrykkelse sammen med Profeterne, sagde de til hverandre: »Hvad gaar der af Kisj's Søn? Er ogsaa Saul iblandt Profeterne?«
Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
12 Saa sagde en der fra Stedet: »Hvem er vel deres Fader?« Derfor blev det et Mundheld: »Er ogsaa Saul iblandt Profeterne?«
Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
13 Da hans profetiske Henrykkelse var ovre, gik han til Gibea.
Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
14 Sauls Farbroder spurgte da ham og Karlen: »Hvor har I været henne?« Han svarede: »Ude at lede efter Æslerne; og da vi ikke fandt dem, gik vi hen til Samuel.«
Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
15 Da sagde Sauls Farbroder: »Fortæl mig, hvad Samuel sagde til eder!«
Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
16 Saul svarede: »Han fortalte os, at Æslerne var fundet!« Men hvad Samuel havde sagt om Kongedømmet, fortalte han ham ikke.
Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
17 Derpaa stævnede Samuel Folket sammen hos HERREN i Mizpa;
Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
18 og han sagde til Israeliterne: »Saa siger HERREN, Israels Gud: Jeg førte Israel op fra Ægypten og frelste eder af Ægypternes Haand og fra alle de Riger, som plagede eder.
ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
19 Men nu vrager I eders Gud, som var eders Frelser i alle eders Ulykker og Trængsler, og siger: Nej, en Konge skal du sætte over os! Saa træd nu frem for HERRENS Aasyn Stamme for Stamme og Slægt for Slægt!«
Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
20 Derpaa lod Samuel alle Israels Stammer træde frem, og Loddet ramte Benjamins Stamme.
Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
21 Saa lod han Benjamins Stamme træde frem Slægt for Slægt, og Matris Slægt ramtes. Saa lod han Matris Slægt træde frem Mand for Mand, og Saul, Kisj's Søn, ramtes. Men da man ledte efter ham, var han ikke til at finde.
Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
22 Da adspurgte de paa ny HERREN: »Er Manden her?« Og HERREN svarede: »Se, han holder sig skjult ved Trosset.«
Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
23 Saa løb de hen og hentede ham der; og da han traadte ind imellem Folket, var han et Hoved højere end alt Folket.
Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
24 Da sagde Samuel til hele Folket: »Ser I ham, HERREN har udvalgt? Hans Lige findes ikke i alt Folket!« Og hele Folket brød ud i Jubelskrig og raabte: »Kongen leve!«
Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
25 Derpaa fremsagde Samuel Kongedømmets Ret for Folket og optegnede den i en Bog, som han lagde hen for HERRENS Aasyn. Saa lod Samuel hele Folket gaa hver til sit:
Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
26 ogsaa Saul gik til sit Hjem i Gibea, og de tapre Mænd, hvis Hjerte Gud rørte, gik med ham.
Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
27 Men nogle Niddinger sagde: »Hvor skulde denne kunne hjælpe os?« Og de ringeagtede ham og bragte ham ingen Hyldingsgave. Men han var, som han var døv.
Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.

< 1 Samuel 10 >