< 1 Peter 2 >

1 Derfor aflægger al Ondskab og al Svig og Hykleri og Avind og al Bagtalelse,
Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
2 og higer som nyfødte Børn efter Ordets uforfalskede Mælk, for at I kunne vokse ved den til Frelse,
Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
3 om I da have smagt, at Herren er god.
yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
4 Kommer til ham, den levende Sten, der vel er forkastet af Menneskene, men er udvalgt og dyrebar for Gud,
Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
5 og lader eder selv som levende Stene opbygge som et aandeligt Hus, til et helligt Præsteskab, til at frembære aandelige Ofre, velbehagelige for Gud ved Jesus Kristus.
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
6 Thi det hedder i et Skriftsted: „Se, jeg lægger i Zion en Hovedhjørnesten, som er udvalgt og dyrebar; og den, som tror paa ham, skal ingenlunde blive til Skamme.”
Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
7 Eder altsaa, som tro, hører Æren til; men for de vantro er denne Sten, som Bygningsmændene forkastede, bleven til en Hovedhjørnesten og en Anstødssten og en Forargelses Klippe;
A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
8 og de støde an, idet de ere genstridige imod Ordet, hvortil de ogsaa vare bestemte.
kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
9 Men I ere en udvalgt Slægt, et kongeligt Præsteskab, et helligt Folk, et Folk til Ejendom, for at I skulle forkynde hans Dyder, som kaldte eder fra Mørke til sit underfulde Lys,
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
10 I, som fordum ikke vare et Folk, men nu ere Guds Folk, I, som ikke fandt Barmhjertighed, men nu have fundet Barmhjertighed.
Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
11 I elskede! jeg formaner eder som fremmede og Udlændinge til at afholde eder fra kødelige Lyster, som jo føre Krig imod Sjælen,
Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
12 saa I føre en god Vandel iblandt Hedningerne, for at de paa Grund af de gode Gerninger, som de faa at se, kunne prise Gud paa Besøgelsens Dag for det, som de bagtale eder for som Ugerningsmænd.
Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
13 Underordner eder under al menneskelig Ordning for Herrens Skyld, være sig en Konge som den højeste,
Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
14 eller Landshøvdinger som dem, der sendes af ham til Straf for Ugerningsmænd, men til Ros for dem, som gøre det gode.
ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
15 Thi saaledes er det Guds Villie, at I ved at gøre det gode skulle bringe de uforstandige Menneskers Vankundighed til at tie;
Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
16 som frie, og ikke som de, der have Friheden til Ondskabs Skjul, men som Guds Tjenere.
Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
17 Ærer alle, elsker Broderskabet, frygter Gud, ærer Kongen!
Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
18 I Trælle! underordner eder under eders Herrer i al Frygt, ikke alene de gode og milde, men ogsaa de urimelige.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
19 Thi dette finder Yndest, dersom nogen, bunden til Gud i sin Samvittighed, udholder Genvordigheder, skønt han lider uretfærdigt.
Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
20 Thi hvad Ros er det, om I holde ud, naar I synde og derfor faa Næveslag? Men dersom I holde ud, naar I gøre det gode og lide derfor, dette finder Yndest hos Gud.
Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
21 Thi dertil bleve I kaldede, efterdi ogsaa Kristus har lidt for eder, efterladende eder et Forbillede, for at I skulle følge i hans Fodspor,
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22 han, som ikke gjorde Synd, ikke heller blev der fundet Svig i hans Mund,
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23 han, som ikke skældte igen, da han blev udskældt, ikke truede, da han led, men overgav det til ham, som dømmer retfærdigt,
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24 han, som selv bar vore Synder paa sit Legeme op paa Træet, for at vi, afdøde fra vore Synder, skulle leve for Retfærdigheden, han, ved hvis Saar I ere blevne lægte.
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
25 Thi I vare vildfarende som Faar, men ere nu vendte om til eders Sjæles Hyrde og Tilsynsmand.
Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.

< 1 Peter 2 >