< Første Kongebog 19 >

1 Akab fortalte nu Jesabel alt, hvad Elias havde gjort, og hvorledes han havde ihjelslaaet alle Profeterne med Sværd,
Ahab fa ya faɗa wa Yezebel kome da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe dukan annabawan da takobi.
2 og Jesabel sendte et Sendebud til Elias og lod sige: »Guderne ramme mig baade med det ene og det andet, om jeg ikke i Morgen ved denne Tid handler med dit Liv, som der er handlet med deres!«
Saboda haka Yezebel ta aika da ɗan aika wa Iliya yă faɗa masa, “Bari alloli su hukunta ni da tsanani, in war haka gobe ban mai da ranka kamar na ɗaya daga cikin annabawan Ba’al ba.”
3 Da blev han bange, stod op og drog bort for at redde sit Liv. Han kom da til Be'ersjeba i Juda. Der lod han sin Tjener blive
Iliya ya ji tsoro, ya gudu don yă ceci ransa. Sa’ad da ya kai Beyersheba a Yahuda, sai ya bar bawansa a can.
4 og vandrede selv en Dagsrejse ud i Ørkenen og satte sig under en Gyvelbusk og ønskede sig Døden, idet han sagde: »Nu er det nok, HERRE; tag mit Liv, thi jeg er ikke bedre end mine Fædre!«
Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
5 Saa lagde han sig til at sove under en Gyvelbusk. Og se, en Engel rørte ved ham og sagde: »Staa op og spis!«
Sa’an nan ya kwanta a ƙarƙashin itacen ya yi barci. Farat ɗaya sai wani mala’ika ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci.”
6 Og da han saa sig om, se, da laa der, hvor hans Hoved havde hvilet, et ristet Brød, og der stod en Krukke Vand; og han spiste og drak og lagde sig igen.
Ya duba kewaye, sai ga wainar burodi kusa da kansa a bisa garwashin wuta mai zafi, da kuma tulun ruwa. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya sāke kwanta.
7 Men HERRENS Engel kom atter og rørte ved ham og sagde: »Staa op og spis, ellers bliver Vejen dig for lang!«
Mala’ikan Ubangiji ya sāke dawowa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za tă yi maka yawa.”
8 Da stod han op og spiste og drak; og styrket af dette Maaltid vandrede han i fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter lige til Guds Bjerg Horeb.
Saboda haka ya tashi ya ci, ya kuma sha. Ta wurin ƙarfin da ya samu saboda wannan abinci, ya yi tafiya yini arba’in da dare arba’in, sai da ya kai Horeb, dutsen Allah.
9 Der gik han ind i en Hule og overnattede. Da lød HERRENS Ord til ham: »Hvad er du her efter, Elias?«
A can ya shiga kogo ya kwana. Sai maganar Ubangiji ta zo masa, ta ce, “Me kake yi a nan, Iliya?”
10 Han svarede: »Jeg har været fuld af Nidkærhed for HERREN, Hærskarers Gud, fordi Israeliterne har forladt din Pagt; dine Altre har de nedbrudt, og dine Profeter har de ihjelslaaet med Sværd! Jeg alene er tilbage, og nu staar de mig efter Livet!«
Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
11 Da sagde han: »Gaa ud og stil dig paa Bjerget for HERRENS Aasyn!« Og se, HERREN gik forbi, og et stort og stærkt Vejr, der sønderrev Bjerge og sprængte Klipper, gik foran HERREN, men HERREN var ikke i Vejret. Efter Vejret kom der et Jordskælv, men HERREN var ikke i Jordskælvet.
Sai Ubangiji ya ce, “Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa.” Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.
12 Efter Jordskælvet kom der Ild, men HERREN var ikke i Ilden. Men efter Ilden kom der en stille, sagte Susen,
Bayan girgizar ƙasa, sai ga wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wuta. Bayan wutar kuma sai ga wata’yar murya.
13 og da Elias hørte den, hyllede han sit Hoved i sin Kappe og gik ud og stillede sig ved Indgangen til Hulen; og se, en Røst lød til ham: »Hvad er du her efter Elias?«
Sa’ad da Iliya ya ji ta, ya ja mayafinsa ya rufe fuskarsa, ya fita ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?”
14 Han svarede: »Jeg har været fuld af Nidkærhed for HERREN, Hærskarers Gud, fordi Israeliterne har forladt din Pagt; dine Altre har de nedbrudt, og dine Profeter har de ihjelslaaet med Sværd! Jeg alene er tilbage, og nu staar de mig efter Livet!«
Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
15 Da sagde HERREN til ham: »Vend tilbage ad den Vej, du kom, og gaa til Ørkenen ved Damaskus; gaa saa hen og salv Hazael til Konge over Aram,
Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka koma ta hanyar da ka zo, ka tafi Hamadan Damaskus. Sa’ad da ka kai can, ka shafe Hazayel yă zama sarki bisa Aram.
16 salv Jehu, Nimsjis Søn, til Konge over Israel og salv Elisa, Sjafats Søn, fra Abel-Mehola til Profet i dit Sted!
Ka kuma shafe Yehu ɗan Nimshi yă zama sarkin Isra’ila, ka shafe Elisha ɗan Shafat daga Abel-Mehola yă gāje ka a matsayin annabi.
17 Den, der undslipper Hazaels Sværd, skal Jehu dræbe, og den, der undslipper Jehus Sværd, skal Elisa dræbe.
Yehu zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Hazayel, Elisha kuwa zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Yehu.
18 Jeg vil lade syv Tusinde blive tilbage i Israel, hvert Knæ, der ikke har bøjet sig for Ba'al, og hver Mund, der ikke har kysset ham.«
Duk da haka zan bar mutane dubu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su rusuna da gwiwansu wa Ba’al ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”
19 Saa gik han derfra; og han traf Elisa, Sjafats Søn, i Færd med at pløje; tolv Spand Okser havde han foran sig, og selv var han ved det tolvte. Da nu Elias gik forbi ham, kastede han sin Kappe over ham.
Sai Iliya ya tafi daga can ya sami Elisha ɗan Shafat, yana noma da shanu goma sha biyu masu garman noma, shi kansa yana jan na goma sha biyun. Iliya ya tafi wurinsa ya jefa mayafinsa a kan Elisha.
20 Saa forlod han Okserne og løb efter Elias og sagde: »Lad mig først kysse min Fader og min Moder, saa vil jeg følge dig!« Han svarede: »Gaa kun tilbage, thi hvad er det ikke, jeg har gjort ved dig!«
Sai Elisha ya bar shanun, ya ruga ya bi Iliya. Ya ce, “Bari in sumbace mahaifina da mahaifiyata, in yi musu bankwana, sa’an nan in zo in bi ka.” Iliya ya ce, “Koma! Me na yi maka?”
21 Da forlod han ham og vendte tilbage; saa tog han og slagtede Oksespandet, kogte Okserne ved Stavtøjet og gav Folkene dem at spise; derpaa brød han op og fulgte Elias og gik ham til Haande.
Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.

< Første Kongebog 19 >