< Første Kongebog 15 >
1 I Kong Jeroboams, Nebats Søns, attende Regeringsaar blev Abija Konge over Juda.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 Tre Aar herskede han i Jerusalem. Hans Moder hed Ma'aka og var en Datter af Absalom.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 Han vandrede i alle de Synder, hans Fader havde begaaet før ham, og hans Hjerte var ikke helt med HERREN hans Gud som hans Fader Davids.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 Men for Davids Skyld lod HERREN hans Gud ham faa en Lampe i Jerusalem, idet han ophøjede hans Sønner efter ham og lod Jerusalem bestaa,
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 fordi David havde gjort, hvad der var ret i HERRENS Øjne, og ikke, saa længe han levede, var veget fra noget af, hvad han havde paalagt ham, undtagen over for Hetiten Urias.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 (Rehabeam laa i Krig med Jeroboam, saa længe han levede).
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 Hvad der ellers er at fortælle om Abija, alt, hvad han gjorde, staar jo optegnet i Judas Kongers Krønike. Abija og Jeroboam laa i Krig med hinanden.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 Saa lagde Abija sig til Hvile hos sine Fædre, og man jordede ham i Davidsbyen; og hans Søn Asa blev Konge i hans Sted.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 I Kong Jeroboam af Israels tyvende Regeringsaar blev Asa Konge over Juda,
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 og han herskede een og fyrretyve Aar i Jerusalem. Hans Moder hed Ma'aka og var en Datter af Absalom.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 Asa gjorde, hvad der var ret i HERRENS Øjne, ligesom hans Fader David;
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 han jog Mandsskøgerne ud af Landet og fjernede alle Afgudsbillederne, som hans Fædre havde ladet lave.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 Han fratog endog sin Moder Ma'aka Værdigheden som Herskerinde, fordi hun havde ladet lave et Skændselsbillede til Ære for Asjera; Asa lod hendes Skændselsbillede nedbryde og brænde i Kedrons Dal.
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 Vel forsvandt Offerhøjene ikke, men alligevel var Asas Hjerte helt med HERREN, saa længe han levede.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 Og han bragte sin Faders og sine egne Helliggaver ind i HERRENS Hus, Sølv, Guld og forskellige Kar.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 Asa og Kong Ba'sja af Israel laa i Krig med hinanden, saa længe de levede.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 Kong Ba'sja af Israel drog op imod Juda og befæstede Rama for at hindre, at nogen af Kong Asa af Judas Folk drog ud og ind.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 Da tog Asa alt det Sølv og Guld, der var tilbage i Skatkamrene i HERRENS Hus og i Kongens Palads, overgav det til sine Folk og sendte dem til Kong Benhadad af Aram, en Søn af Hezjons Søn Tabrimmon, som boede i Damaskus, idet han lod sige:
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 »Der bestaar en Pagt mellem mig og dig, mellem min Fader og din Fader; her sender jeg dig en Gave af Sølv og Guld; bryd derfor din Pagt med Kong Ba'sja af Israel, saa at han nødes til at drage bort fra mig!«
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 Benhadad gik ind paa Kong Asas Forslag og sendte sine Hærførere mod Israels Byer og indtog Ijjon, Dan, Abel-Bet-Ma'aka og hele Kinnerot tillige med hele Naftalis Land.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 Da Ba'sja hørte det, opgav han at befæste Rama og vendte tilbage til Tirza.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Men Kong Asa stævnede hver eneste Mand i hele Juda sammen, og de førte Stenene og Træværket bort, som Ba'sja havde brugt ved Befæstningen af Rama; dermed befæstede Kong Asa saa Geba i Benjamin og Mizpa.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 Hvad der ellers er at fortælle om Asa, alle hans Heltegerninger, alt, hvad han gjorde, og de Byer, han befæstede, staar jo optegnet i Judas Kongers Krønike. I øvrig led han i sin Alderdom af en Sygdom i Fødderne.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 Saa lagde han sig til Hvile hos sine Fædre og blev jordet hos sine Fædre i sin Fader Davids By; og hans Søn Josafat blev Konge i hans Sted.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 Nadab, Jeroboams Søn, blev Konge over Israel i Kong Asa af Judas andet Regeringsaar, og han herskede to Aar over Israel.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, og vandrede i sin Faders Spor og i de Synder, han havde forledt Israel til.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 Da stiftede Ba'sja, Ahijas Søn af Issakars Hus, en Sammensværgelse imod ham, og Ba'sja huggede ham ned ved Gibbeton, der tilhørte Filisterne, medens Nadab og hele Israel belejrede Byen.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 Ba'sja dræbte ham i Kong Asa af Judas tredje Regeringsaar og blev Konge i hans Sted;
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 nu da han var blevet Konge, lod han hele Jeroboams Hus nedhugge, idet han ikke skaanede en eneste Sjæl af Jeroboams Slægt, men udryddede dem efter det Ord, HERREN havde talet ved sin Tjener Ahija fra Silo,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 for de Synders Skyld, Jeroboam havde begaaet og forledt Israel til, for den Krænkelse, han havde tilføjet HERREN, Israels Gud.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 Hvad der ellers er at fortælle om Nadab, alt, hvad han gjorde, staar jo optegnet i Israels Kongers Krønike.
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 (Asa og Kong Ba'sja af Israel laa i Krig med hinanden, saa længe de levede.)
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 I Kong Asa af Judas tredje Regeringsaar blev Ba'sja, Ahijas Søn, Konge over hele Israel, og han herskede tre og tyve Aar i Tirza.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, og vandrede i Jeroboams Spor og de Synder, han havde forledt Israel til.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.