< 1 Johannes 2 >

1 Mine Børn! dette skriver jeg til eder, for at I ikke skulle synde. Og dersom nogen synder, have vi en Talsmand hos Faderen, Jesus Kristus, den retfærdige,
'Ya'yana, na rubuta ma ku wadannan abubuwa domin kada kuyi zunubi. Amma idan wani yayi zunubi muna da matsakanci a wurin Uba, Yesu Almasihu, mai adalci.
2 og han er en Forsoning for vore Synder, dog ikke alene for vore, men ogsaa for hele Verdens.
Shine fansar zunubanmu, ba ma namu kadai ba amma na duniya dukka.
3 Og derpaa kende vi, at vi have kendt ham, om vi holde hans Bud.
Ta haka muka san cewa mun san shi, idan mun kiyaye dokokinsa.
4 Den, som siger: „Jeg kender ham,” og ikke holder hans Bud, han er en Løgner, og i ham er Sandheden ikke;
Duk wanda yace, “Na san Allah” amma bai kiyaye dokokinsa ba, makaryaci ne gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
5 men den, som holder hans Ord, i ham er sandelig Guds Kærlighed fuldkommet. Derpaa kende vi, at vi ere i ham.
Amma duk wanda ya kiyaye maganarsa, hakika kaunar Allah ta kammala a cikin wannan mutum. Ta wurin haka muka sani muna cikinsa.
6 Den, som siger, at han bliver i ham, han er ogsaa skyldig selv at vandre saaledes, som han vandrede.
Duk wanda yace yana cikin Allah dole ne shi da kansa yayi tafiya kamar yadda Yesu Almasihu yayi.
7 I elskede, jeg skriver til eder ikke et nyt Bud, men et gammelt Bud, som I have haft fra Begyndelsen. Det gamle Bud er det Ord, som I have hørt.
Kaunatattu, ba sabuwar doka nike rubuta maku ba, amma tsohuwar doka ce wadda kuka ji tun farko. Tsohuwar dokar kuwa itace maganar da kuka ji tun farko.
8 Og dog skriver jeg til eder et nyt Bud, hvilket er sandt i ham og i eder, thi Mørket drager bort, og det sande Lys skinner allerede.
Amma yanzu ina rubuta maku sabuwar doka wadda gaskiya ce a cikin Almasihu da cikinku, saboda duhu yana wucewa, haske na gaskiya yana haskakawa.
9 Den, som siger, at han er i Lyset, og hader sin Broder, han er i Mørket endnu.
Duk wanda yace yana cikin haske amma yana kin dan'uwansa, yana cikin duhu har yanzu.
10 Den, som elsker sin Broder, bliver i Lyset, og der er ingen Forargelse i ham.
kuma wanda yake kaunar dan'uwansa yana cikin haske babu dalilin tuntube a wurinsa.
11 Men den, som hader sin Broder, er i Mørket og vandrer i Mørket, og han ved ikke, hvor han gaar hen, fordi Mørket har blindet hans Øjne.
Amma duk wanda yake kin dan'uwansa yana cikin duhu, yana kuma tafiya cikin duhu, bai san ma inda ya nufa ba, domin duhu ya makantar da shi.
12 Jeg skriver til eder, mine Børn! fordi eders Synder ere eder forladte for hans Navns Skyld.
Na rubuta maku, ya ku kaunatun 'ya'yana, saboda an gafarta zunubanku domin sunansa.
13 Jeg skriver til eder, I Fædre! fordi I kende ham, som er fra Begyndelsen. Jeg skriver til eder, I unge! fordi I have overvundet den onde. Jeg har skrevet til eder, mine Børn! fordi I kende Faderen.
Na rubuta maku, ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku matasa saboda kun yi nasara da mugun. Na rubuta maku, yara kanana, saboda kun san Uban.
14 Jeg har skrevet til eder, I Fædre! fordi I kende ham, som er fra Begyndelsen. Jeg har skrevet til eder, I unge! fordi I ere stærke, og Guds Ord bliver i eder, og I have overvundet den onde.
Na rubuta maku, Ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku, matasa, saboda kuna da karfi, kuma maganar Allah tana zaune cikinku. Kuma kun yi nasara da mugun.
15 Elsker ikke Verden, ikke heller de Ting, som ere i Verden! Dersom nogen elsker Verden, er Faderens Kærlighed ikke i ham.
Kada kuyi kaunar duniya ko abubuwan da suke cikin duniya. Idan wani yayi kaunar duniya, kaunar Uban bata cikinsa.
16 Thi alt det, som er i Verden, Kødets Lyst og Øjnenes Lyst og Livets Hoffærdighed, er ikke af Faderen, men af Verden.
Domin dukkan abubuwan da suke a cikin duniya, kwadayi na jiki, abin da idanu suke sha'wa, da rayuwar girman kai ta wofi, ba na Uban bane amma na duniya ne.
17 Og Verden forgaar og dens Lyst; men den, som gør Guds Villie, bliver til evig Tid. (aiōn g165)
Duniya tana wucewa tare da sha'awarta. Amma dukkan wanda ya aikata nufin Allah zaya kasance har abada. (aiōn g165)
18 Mine Børn! det er den sidste Time, og som I have hørt, at Antikrist kommer, saaledes ere nu mange Antikrister fremtraadte; deraf kende vi, at det er den sidste Time.
Yara kanana, sa'a ta karshe ce. Kamar dai yadda kuka ji magafcin Almasihu yana zuwa, ko yanzu ma magaftan Almasihu da yawa sun rigaya sun zo, ta haka muka san sa'a ta karshe ce.
19 De ere udgaaede fra os, men de vare ikke af os; thi dersom de havde været af os, da vare de blevne hos os. Dog, det var, for at det skulde blive aabenbart, at de ikke alle ere af os.
Sun fita daga cikinmu, dama su bana cikinmu bane. Gama idan da su namu ne da sun ci gaba tare damu. Amma da yake sun fita, ya nuna su ba na cikinmu bane.
20 Og I have Salvelse fra den hellige og vide alt.
Amma ku kun karbi shafewa daga wurin Mai Tsarki, kuma dukkanku kun san gaskiya.
21 Jeg har ikke skrevet til eder, fordi I ikke vide Sandheden; men fordi I vide den og vide, at ingen Løgn er af Sandheden.
Bana rubuta maku bane domin baku san gaskiya ba, amma saboda kun santa, kuma ba wata karya da ta fito daga gaskiya.
22 Hvem er Løgneren uden den, som nægter, at Jesus er Kristus? Denne er Antikristen, som fornægter Faderen og Sønnen.
Wanene makaryaci shine wanda yayi musu cewa Yesu ba Almasihu bane? Wannan mutumin shi ne magafcin Almasihu, tun da yayi musun Uba yayi musun Dan.
23 Hver den, som fornægter Sønnen, har ej heller Faderen; den, som bekender Sønnen, har ogsaa Faderen.
Ba wanda yayi musun Dan kuma yake da Uban. Dukkan wanda ya amince da Dan yana da Uban ma.
24 Hvad I have hørt fra Begyndelsen, det blive i eder! Dersom det, som I have hørt fra Begyndelsen, bliver i eder, skulle ogsaa I blive i Sønnen og i Faderen.
A game daku kuma, sai ku bari abinda kuka ji daga farko ya zauna a cikinku. Idan abin da kuka ji daga farko ya zauna a cikinku, kuma zaku kasance a cikin Dan da kuma Uban.
25 Og dette er den Forjættelse, som han selv tilsagde os, det evige Liv. (aiōnios g166)
Alkawarin da ya bamu kenan, rai na har abada. (aiōnios g166)
26 Dette har jeg skrevet til eder om dem, som forføre eder.
Na rubuta maku wadannan abubuwa ne game da wadanda zasu baudar daku.
27 Og den Salvelse, som I fik af ham, bliver i eder, og I have ikke nødig, at nogen skal lære eder; men saaledes som hans Salvelse lærer eder alt, er det ogsaa sandt og er ikke Løgn, og som den har lært eder, skulle I blive i ham.
Game daku, shafewar daku ka samu daga wurinsa tana nan a cikinku, baku bukatar wani ya koyar daku. Amma kamar yadda shafewar da kuka karba a wurinsa ta koya maku dukkan abu, kuma gaskiya ne ba karya bane, tana nan a cikinku kamar yadda a ka koya maku, ku kasance a cikinsa.
28 Og nu mine Børn! bliver i ham, for at vi, naar han aabenbares, kunne have Frimodighed og ikke skulle blive til Skamme for ham ved hans Tilkommelse.
Yanzu fa, 'ya'ya na kaunatattu, ku kasance a cikinsa domin sa'adda zai baiyyana mu zama da gabagadi ba tare da kunya ba a gabansa sa'adda zai zo.
29 Dersom I vide, at han er retfærdig, da erkender, at hver den, som gør Retfærdighed, er født af ham.
Idan kun sani shi mai adalci ne, kun sani dukkan wanda ke aikata adalci haifaffe ne daga wurinsa.

< 1 Johannes 2 >