< Første Krønikebog 21 >

1 Satan traadte op mod Israel og æggede David til at holde Mandtal over Israel.
Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
2 David sagde da til Joab og Hærførerne: »Drag ud og tæl Israel fra Be'ersjeba til Dan og bring mig Efterretning, for at jeg kan faa Tallet paa dem at vide!«
Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
3 Men Joab svarede: »Maatte HERREN forøge sit Folk hundredfold! Er de ikke, Herre Konge, min Herres Trælle alle sammen? Hvorfor vil min Herre det? Hvorfor skal det blive Israel til Skyld?«
Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
4 Men Joab maatte bøje sig for Kongens Ord, og Joab begav sig derfor bort, drog hele Israel rundt og kom tilbage til Jerusalem.
Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
5 Joab opgav derpaa David Tallet, der var fundet ved Folketællingen, og hele Israel talte 1 100 000 kraftige Mænd, Juda 470 000.
Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
6 Men Levi og Benjamin havde han ikke talt med, thi Kongens Ord var Joab en Gru.
Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
7 Dette var ondt i Guds Øjne, og han slog Israel.
Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
8 Da sagde David til Gud: »Jeg har syndet svarlig i, hvad jeg har gjort. Men tilgiv nu din Tjeners Brøde, thi jeg har handlet som en stor Daare!«
Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
9 Men HERREN talede saaledes til Gad, Davids Seer:
Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
10 »Gaa hen og sig saaledes til David: Saa siger HERREN: Jeg forelægger dig tre Ting; vælg selv, hvilken jeg skal lade times dig!«
“Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
11 Gad kom da til David og sagde til ham: »Saa siger HERREN: Vælg!
Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
12 Vælger du tre Hungersnødsaar, eller vil du i tre Maaneder flygte for dine Fjender og dine Avindsmænds Sværd, eller skal der komme tre Dage med HERRENS Sværd og Pest i Landet, i hvilke HERRENS Engel spreder Ødelæggelse i hele Israels Omraade? Se nu til, hvad jeg skal svare ham, der har sendt mig!«
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
13 David svarede Gad: »Jeg er i saare stor Vaande — lad mig saa falde i HERRENS Haand, thi hans Barmhjertighed er saare stor; i Menneskehaand vil jeg ikke falde!«
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
14 Saa sendte HERREN Pest over Israel, og af Israel døde 70 000 Mennesker.
Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
15 Og Gud sendte en Engel til Jerusalem for at ødelægge det. Men lige som han skulde til at ødelægge Byen, saa HERREN til og angrede det onde; og han sagde til Engelen, som var ved at ødelægge: »Nu er det nok, drag din Haand tilbage!« HERRENS Engel stod da ved Jebusiten Ornans Tærskeplads.
Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
16 Da David løftede sit Blik og saa HERRENS Engel staa mellem Himmel og Jord med draget Sværd i Haand, rettet mod Jerusalem, faldt han og de Ældste, der var klædt i Sæk, paa deres Ansigt;
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
17 og David sagde til Gud: »Var det ikke mig, der sagde, at Folket skulde tælles? Det er mig, der har syndet, og saare ilde har jeg handlet; men Faarene der, hvad har de gjort? HERRE min Gud, lad din Haand dog ramme mig og mit Fædrenehus, men lad Plagen ikke ramme dit Folk!«
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
18 Da sagde HERRENS Engel til Gad, at han skulde byde David gaa op og rejse HERREN et Alter paa Jebusiten Ornans Tærskeplads.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
19 Og David gik derop, efter det Ord Gad havde talt i HERRENS Navn.
Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
20 Da Ornan vendte sig om, saa han Kongen og hans fire Sønner, der var hos ham, komme gaaende. Ornan var ved at tærske Hvede.
Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
21 Og David naaede hen til Ornan, og da Ornan saa op og fik Øje paa David, forlod han Tærskepladsen og kastede sig paa sit Ansigt til Jorden for ham.
Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
22 Da sagde David til Ornan: »Overlad mig din Tærskeplads, for at jeg der kan bygge HERREN et Alter! For fuld betaling skal du overlade mig den, at Folket maa blive friet fra Plagen!«
Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
23 Da sagde Ornan til David: »Min Herre Kongen tage den og gøre, hvad ham tykkes ret; se, jeg giver Okserne til Brændofre, Tærskeslæderne til Brændsel og Hveden til Afgrødeoffer; jeg giver det hele!«
Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
24 Men Kong David svarede Ornan: »Nej, jeg vil købe det for fuld Betaling, thi til HERREN vil jeg ikke tage, hvad dit er, eller bringe et Brændoffer, som intet koster mig!«
Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
25 Saa gav David Ornan Guld til en Vægt af 600 Sekel for Pladsen;
Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
26 og David byggede HERREN et Alter der og ofrede Brændofre og Takofre; og da han raabte til HERREN, svarede HERREN ham ved at lade Ild falde ned fra Himmelen paa Brændofferalteret,
Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
27 Og paa HERRENS Bud stak Engelen sit Sværd i Balgen igen.
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
28 Paa den Tid ofrede David paa Jebusiten Ornans Tærskeplads, fordi han havde set, at HERREN havde svaret ham der;
A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
29 men HERRENS Bolig, som Moses havde rejst i Ørkenen, og Brændofferalteret stod paa den Tid paa Offerhøjen i Gibeon.
Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
30 Men David kunde ikke gaa hen og søge Gud foran Alteret, thi han var rædselsslagen over HERRENS Engels Sværd.
Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.

< Første Krønikebog 21 >