< Zefanias 1 >
1 Herrens Ord, som kom til Zefanias, en Søn af Kusi, der var en Søn af Gedalia, der var en Søn af Amaria, der var en Søn af Ezekias, i de Dage, da Josias, Amons Søn, var Konge i Juda.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 Bort, ja, bort vil jeg tage alt af Jorden, siger Herren.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 Jeg, vil borttage Mennesker og Dyr, borttage Fuglene under Himmelen og Fiskene i Havet og alle Anstød tillige med de ugudelige; og jeg vil udrydde Menneskene af Jorden, siger Herren.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 Og jeg vil udstrække min Haand imod Juda og imod alle Jerusalems Indbyggere, og jeg vil udrydde af dette Sted det overblevne af Baal, Afgudspræsternes Navn tillige med Præsterne;
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 og dem, som paa Tagene tilbede Himmelens Hær, og dem, som tilbedende sværge til Herren og dog sværge ved deres Konge;
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 og dem, som ere vegne bort fra Herren, og som ikke have søgt Herren og ikke spurgt efter ham.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Stille for den Herre, Herre! thi Herrens Dag er nær; thi Herren har beredt en Offerslagtning, han har helliget sine indbudne.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 Og det skal ske paa Herrens Offerslagtnings Dag, at jeg vil hjemsøge Fyrsterne og Kongens Børn og alle, som klæde sig i fremmed Dragt.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 Og jeg vil hjemsøge paa den Dag hver den, som springer over Dørtærskelen, dem, som fylde deres Herres Hus med Vold og Svig.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 Og der skal paa denne Dag, siger Herren, lyde Raab fra Fiskeporten og Hylen fra Stadens anden Del og stor Forstyrrelse fra Højene.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Hyler, I som bo i Morteren! thi alt Kræmmerfolket er tilintetgjort, alle de, som vare belæssede med Sølv, ere udryddede.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 Og det skal ske paa den Tid, at jeg vil ransage Jerusalem med Lygter, og jeg vil hjemsøge de Folk, som ligge stille paa deres Bærme, dem, som sige i deres Hjerte: Herren gør hverken godt eller ondt.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 Og deres Gods skal blive til Rov og deres Huse til Ødelæggelse, og de skulle bygge Huse, men ikke bo i dem, og plante Vingaarde, men ikke drikke Vin af dem.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 Nær er Herrens Dag, den store, den er nær og haster saare; Lyden af Herrens Dag høres; der raaber den vældige bitterlig.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 En Vredes Dag er denne Dag, en Nøds og Trængsels Dag, en Forstyrrelses og Ødelæggelses Dag, en Mørkheds og Dunkelheds Dag, en Skys og Mulms Dag,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 en Trompetklangs og Krigsraabs Dag over de befæstede Stæder og over de høje Hjørnetaarne.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 Og jeg vil ængste Menneskene, og de skulle gaa som blinde; thi de have syndet imod Herren; og deres Blod skal udøses som Støv og deres Kød som Skarn.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Hverken deres Sølv eller deres Guld skal kunne redde dem paa Herrens Vredes Dag, men ved hans Nidkærheds Ild skal den hele Jord fortæres; thi han skal gøre Ende, ja, hastelig gøre Ende paa alle Jordens Beboere.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.