< Zakarias 1 >
1 I den ottende Maaned, i Darius's andet Aar, kom Herrens Ord til Profeten Sakarias, en Søn af Berekias, en Sønnesøn af Iddo, saaledes:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 Herren har været højlig fortørnet paa eders Fædre.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Og du skal sige til dem: Saa siger den Herre Zebaoth: Vender om til mig, siger den Herre Zebaoth, saa vil jeg vende om til eder, siger den Herre Zebaoth.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Værer ikke som eders Fædre, til hvilke de forrige Profeter raabte og sagde: Saa siger den Herre Zebaoth: Vender dog om fra eders onde Veje og eders onde Idrætter; men de hørte ikke og gave ikke Agt paa mig, siger Herren.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Eders Fædre, hvor ere de? og Profeterne, mon de leve til evig Tid?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Dog, mine Ord og mine Bestemmelser, som jeg meddelte mine Tjenere, Profeterne, have de ikke rammet eders Fædre, saa de vendte om og sagde: Ligesom den Herre Zebaoth havde tænkt at gøre imod os efter vore Veje og efter vore Idrætter, saaledes har han gjort imod os.
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 Paa den fire og tyvende Dag i den ellevte Maaned, det er Maaneden Sebat, i Darius's andet Aar, kom Herrens Ord til Profeten Sakarias, Berekias's Søn, Iddos Sønnesøn, saaledes:
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 Jeg saa om Natten, og se, en Mand, der red paa en rød Hest, og han holdt stille imellem Myrtetræerne, som vare i Dalen, og bag ham var der røde, graa og hvide Heste.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 Og jeg sagde: Hvad betyde disse, min Herre? Og Engelen, som talte med mig, sagde til mig: Jeg vil lade dig se, hvad disse betyde.
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 Og den Mand, som holdt stille imellem Myrtetræerne, svarede og sagde: Det er dem, som Herren har sendt til at vandre Jorden rundt.
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 Og de svarede Herrens Engel, som stod imellem Myrtetræerne, og sagde: Vi have vandret Jorden rundt, og se, hele Jorden nyder Ro og Hvile.
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 Da svarede Herrens Engel og sagde: Herre Zebaoth! hvor længe varer det, inden du vil forbarme dig over Jerusalem og over Judas Stæder, paa hvilke du har været vred nu i halvfjerdsindstyve Aar?
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 Og Herren svarede Engelen, som talte med mig, med gode Ord, med trøstende Ord.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 Og Engelen, som talte med mig, sagde til mig: Raab og sig: Saa siger den Herre Zebaoth: Jeg har været nidkær for Jerusalem og for Zion med en stor Nidkærhed.
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 Men med en stor Fortørnelse er jeg fortørnet paa Hedningerne, som ere saa trygge; thi da jeg en liden Stund havde været fortørnet, saa hjalp de til Ulykken.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Derfor, saa siger Herren, har jeg atter vendt mig til Jerusalem med Barmhjertighed, mit Hus skal bygges derudi, siger den Herre Zebaoth, og Maalesnoren skal udstrækkes over Jerusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Raab fremdeles, og sig: Saa siger den Herre Zebaoth: Mine Stæder skulle endnu strømme over af gode Ting, og Herren skal endnu trøste Zion og endnu udvælge Jerusalem.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Og jeg opløftede mine Øjne og saa, og se, fire Horn!
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 Og jeg sagde til Engelen, som talte med mig: Hvad betyde disse? og han sagde til mig: Disse ere de Horn, som adspredte Juda, Israel og Jerusalem.
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 Da lod Herren mig se fire Smede.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 Og jeg sagde: Hvad komme disse for at gøre? og han sagde: Hine ere de Horn, som adspredte Juda paa den Maade, at ingen opløftede sit Hoved; men saa kom disse for at forfærde dem, for at nedslaa de Hedningers Horn, som rejste Horn imod Judas Land, for at adsprede det.
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”