< Zakarias 2 >

1 Og jeg opløftede mine Øjne og saa, og se, en Mand og en Maalesnor i hans Haand!
Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
2 Og jeg sagde: Hvor gaar du hen? og han sagde til mig: Hen at maale Jerusalem for at se, hvor stor dens Bredde, og hvor stor dens Længde er.
Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
3 Og se, Engelen, som talte med mig, gik ud, og en anden Engel gik ud imod ham.
Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
4 Og han sagde til ham: Løb, tal til denne unge Karl, og sig: Jerusalem skal ligge som aabne Byer, formedelst den Mangfoldighed af Mennesker og Kvæg, som er midt i den.
ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
5 Og jeg, jeg vil være den en Ildmur trindt omkring, siger Herren, og jeg vil være til Herlighed midt i den.
Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
6 Ve! ve! flyr da ud af Nordens Land, siger Herren; thi som Himmelens fire Vejr har jeg udbredet eder, siger Herren.
“Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
7 Ve! Zion, red dig, du, som bor hos Babels Datter!
“Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
8 Thi saa siger den Herre Zebaoth, at han har sendt mig efter Ære ud til Hedningerne, som plyndrede eder; thi den, som rører ved eder, rører ved hans Øjesten.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
9 Thi se, jeg svinger min Haand over dem, og de skulle blive et Bytte for dem, som tjente dem; og I skulle fornemme, at den Herre Zebaoth har sendt mig.
Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
10 Syng og vær glad, du Zions Datter! thi se, jeg kommer og vil bo i din Midte, siger Herren.
“Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
11 Og mange Hedningefolk skulle slutte sig til Herren paa den Dag, og de skulle blive mig et Folk, og jeg vil bo i din Midte, og du skal fornemme, at den Herre Zebaoth har sendt mig til dig.
“Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
12 Og Herren skal tage Juda som sin Del til Eje paa den hellige Jordbund, og han skal fremdeles udvælge Jerusalem.
Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
13 Stille, alt Kød, for Herrens Ansigt; thi han har rejst sig fra sin hellige Bolig.
Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”

< Zakarias 2 >