< Zakarias 10 >
1 Begærer Regn af Herren paa den sildige Regns Tid! Herren skaffer Lyn og giver dem Regnskyl, for enhver Mand Urter paa Marken.
Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
2 Thi Husguderne have talt Falskhed, og Spaamændene have skuet Løgn, og skuffende Drømme tale de, med Forfængelighed trøste de; derfor ere de dragne bort som en Hjord, de ere i Nød, thi der er ingen Hyrde.
Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
3 Imod Hyrderne er min Vrede optændt, og Bukkene vil jeg hjemsøge; thi den Herre Zebaoth har besøgt sin Hjord, Judas Hus, og gjort dem som sin statelige Hest i Krigen.
“Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
4 Derfra skal Hjørnestenen, derfra skal Naglen, derfra skal Krigsbuen være, derfra skal tillige hver streng Hersker udgaa.
Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
5 Og de skulle være som Helte og træde Gadeskarn ned i Krigen, og de skulle stride, thi Herren skal være med dem; og de, som ride paa Heste, skulle beskæmmes.
Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
6 Og jeg vil styrke Judas Hus og frelse Josefs Hus og give dem Bolig; thi jeg har forbarmet mig over dem, og de skulle vorde, som om jeg ikke havde bortkastet dem; thi jeg er Herren deres Gud og vil bønhøre dem.
“Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
7 Og Efraim skal blive som en Helt, og deres Hjerte glædes ligesom af Vin, og deres Børn skulle se det og glæde sig, deres Hjerte skal fryde sig i Herren.
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
8 Jeg vil fløjte ad dem og samle dem; thi jeg har genløst dem, og de skulle blive mangfoldige, ligesom de have været mangfoldige.
Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
9 Og jeg vil saa dem iblandt Folkene, og de skulle ihukomme mig paa de langt fraliggende Steder, og de skulle leve tillige med deres Børn og komme tilbage.
Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
10 Og jeg vil føre dem tilbage fra Ægyptens Land og samle dem fra Assyrien; og jeg vil føre dem til Gileads og Libanons Land, og der skal ikke findes Rum nok for dem.
Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
11 Og han skal gaa igennem Trængselshavet og slaa Bølgerne i Havet, og alle Strømmens Dyb skulle udtørres; og Assyriens Hovmod skal nedtrykkes, og Ægyptens Spir skal vige.
Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
12 Og jeg vil styrke dem i Herren, og i hans Navn skulle de vandre, siger Herren.
Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.