< Rut 4 >

1 Og Boas gik op til Porten og sad der, og se, Løseren gik forbi, som Boas havde talt om, og han sagde til denne: Træd nærmere, sæt dig her, min Ven; og han traadte nærmere og satte sig.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Og han tog ti Mænd af de Ældste i Staden og sagde: Sætter eder her, og de satte sig.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Da sagde han til Løseren: Den Del af Marken, som hørte vor Broder Elimelek til, den har Noomi, som er kommen tilbage af Moabiternes Land, solgt.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Og jeg sagde: Jeg vil aabenbare det for dine Øren, og sige: Køb det i Overværelse af Indbyggerne og de Ældste af mit Folk: Dersom du vil løse det, løs det, men dersom du ikke vil løse det, giv mig det til Kende, at jeg kan vide det; thi der er ingen uden du til at løse det og jeg efter dig; og han sagde: Jeg vil løse det.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Og Boas sagde: Paa hvilken Dag du køber det Land af Noomis Haand, da køber du det og af den moabitiske Ruth, den dødes Hustru, for at oprejse den døde et Navn paa hans Arv.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Da sagde Løseren: Jeg kan ikke løse det for mig, at jeg ikke skal fordærve min egen Arv; løs du det for dig, det jeg skulde løse; thi jeg kan ikke løse det.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Og dette var fordum Sædvane i Israel ved Løsning og ved Skiften til at stadfæste al Handel, at een drog sin Sko af og gav sin Næste; og det var Vidnesbyrdet i Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Og Løseren sagde til Boas: Køb dig det; og han drog sin Sko af.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Da sagde Boas til de Ældste og til alt Folket: I ere Vidner i Dag, at jeg har købt alt det, som hørte Elimelek til, og alt det, som hørte Kiljon og Malon til, af Noomis Haand.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 Og tilmed har jeg taget Ruth den moabitiske, Malons Hustru, mig til en Hustru, til at oprejse den døde et Navn paa hans Arv, at den dødes Navn ikke skal udslettes blandt hans Brødre og af hans Steds Port; dertil ere I Vidner i Dag.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Og alt Folket, som var i Porten, og de Ældste sagde: Vi ere Vidner; Herren give, at den Kvinde, der kommer i dit Hus, maa blive som Rakel og som Lea, hvilke begge byggede Israels Hus; og bliv du mægtig i Efrata og bliv navnkundig i Bethlehem!
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 Og dit Hus vorde ligesom Perez' Hus, hvem Thamar fødte Juda, ved den Sæd, som Herren skal give dig af denne unge Kvinde.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Saa tog Boas Ruth, og hun blev ham til Hustru, og han gik ind til hende, og Herren gav hende, at hun blev frugtsommelig, og hun fødte en Søn.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Da sagde Kvinderne til Noomi: Velsignet være Herren, som ikke vilde lade dig fattes en Løser i Dag, og hans Navn vorde priset i Israel!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 Og han skal være dig til at vederkvæge Sjælen og til at opholde dig i din Alderdom; thi din Sønnekone, som dig elskede, har født ham, hun, som er dig bedre end syv Sønner.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 Og Noomi tog Barnet og lagde det paa sit Skød, og hun blev hans Fostermoder.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 Og Naboerskerne kaldte ham med Navn, sigende: Noomi er født en Søn; de kaldte hans Navn Obed, han var Fader til Isai, Davids Fader.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Og disse ere Perez' Slægter: Perez avlede Hezron,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 og Hezron avlede Ram, og Ram avlede Amminadab,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 og Amminadab avlede Nahesson, og Nahesson avlede Salmon,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 og Salmon avlede Boas, og Boas avlede Obed,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 og Obed avlede Isai, og Isai avlede David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Rut 4 >