< Aabenbaringen 11 >
1 Og der blev givet mig et Rør ligesom en Maalestok, med de Ord: Staa op og maal Guds Tempel og Alteret og dem, som tilbede deri.
Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, “Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa.
2 Men Forgaarden uden for Templet, lad den ude og maal den ikke, thi den er given til Folkeslagene; og de skulle nedtræde den hellige Stad i to og fyrretyve Maaneder.
Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.
3 Og jeg vil give mine tvende Vidner, at de skulle profetere eet Tusinde, to Hundrede og tresindstyve Dage, klædte i Sække.
Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki.
4 Disse ere de tvende Olietræer og de tvende Lysestager, som staa for Jordens Herre.
Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 Og dersom nogen vil gøre dem Skade, udgaar der Ild af deres Mund og fortærer deres Fjender; og dersom nogen vil gøre dem Skade, bør han saaledes ihjelslaas.
Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.
6 Disse have Magt til at lukke Himmelen, saa at der ingen Regn skal falde i deres Profetis Dage; og de have Magt over Vandene til at forvandle dem til Blod og til at slaa Jorden med alskens Plage, saa ofte de ville.
Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama.
7 Og naar de faa fuldendt deres Vidnesbyrd, skal Dyret, som stiger op af Afgrunden, føre Krig imod dem og overvinde dem og ihjelslaa dem. (Abyssos )
Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su. (Abyssos )
8 Og deres Lig skal ligge paa Gaden i den store Stad, som i aandelig Forstand kaldes Sodoma og Ægypten, der, hvor ogsaa deres Herre blev korsfæstet.
Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu.
9 Og Mennesker af alle Folk og Stammer og Tungemaal og Folkeslag skulle se paa deres Lig i tre og en halv Dag og ikke tilstede, at deres Lig lægges i Grav.
Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.
10 Og de, som bo paa Jorden, glæde sig over dem og fryde sig; og de sende hverandre Gaver, fordi disse to Profeter vare til Plage for dem, som bo paa Jorden.
Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya.
11 Og efter de tre og en halv Dags Forløb kom der Livs Aande fra Gud i dem; og de stode paa deres Fødder, og stor Frygt faldt paa dem, som saa dem.
Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu.
12 Og de hørte en høj Røst fra Himmelen, som sagde til dem: Stiger her op! Og de stege op til Himmelen i Skyen, og deres Fjender derpaa.
Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, “Ku hauro nan!” Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.
13 Og i samme Stund skete der et stort Jordskælv, og Tiendedelen af Staden faldt, og syv Tusinde Personer bleve dræbte i Jordskælvet; og de andre bleve forfærdede og gave Himmelens Gud Ære.
A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama.
14 Det andet Ve er til Ende; se, det tredje Ve kommer snart.
Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.
15 Og den syvende Engel basunede, og der hørtes høje Røster i Himmelen, som sagde: Herredømmet over Verden er blevet vor Herres og hans Salvedes, og han skal være Konge i Evighedernes Evigheder. (aiōn )
Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin.” (aiōn )
16 Og de fire og tyve Ældste, som sidde for Guds Aasyn paa deres Troner, faldt ned paa deres Ansigter og tilbade Gud og sagde:
Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada.
17 Vi takke dig, Herre Gud, almægtige, du, som er, og som var, fordi du har taget din store Magt og tiltraadt dit Kongedømme,
Suka ce, “Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.
18 og Folkeslagene vrededes, og din Vrede kom og Tiden til, at de døde skulle dømmes, og til at give Lønnen til dine Tjenere, Profeterne, og de hellige og dem, som frygte dit Navn, de smaa og de store, og til at ødelægge dem, som lægge Jorden øde.
Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya.”
19 Og Guds Tempel i Himmelen blev aabnet, og hans Pagts Ark kom til Syne i hans Tempel, og der kom Lyn og Røster og Tordener og Jordskælv og stærk Hagel.
Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.