< Salme 95 >
1 Kommer, lader os synge med Fryd for Herren, lader os raabe af Glæde for vor Frelses Klippe!
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Lader os komme frem for hans Ansigt med Tak, lader os raabe af Glæde for ham med Psalmer!
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 Thi Herren er en stor Gud, ja, en stor Konge over alle Guder.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 I hans Haand ere Jordens Dybder, og Bjergenes Højder høre ham til.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 Havet er hans, og han har skabt det, og hans Hænder have dannet det tørre Land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Kommer, lader os tilbede og nedbøje os, lader os bøje Knæ for Herren, vor Skabers Ansigt!
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 Thi han er vor Gud, og vi ere det Folk, han føder, og den Hjord, hans Haand leder: Vilde I dog i Dag høre hans Røst!
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Forhærder ikke eders Hjerte, som ved Meriba, som paa den Dag ved Massa udi Ørken,
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 hvor eders Fædre fristede mig; de prøvede mig, og de saa min Gerning.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Fyrretyve Aar kededes jeg ved den Slægt og sagde: De ere et Folk, som farer vild med Hjertet, de kendte ikke mine Veje,
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 saa at jeg svor i min Vrede: De skulle ikke komme til min Hvile!
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”