< Salme 89 >
1 En Undervisning; af Ethan, Esrahiteren. Jeg vil synge om Herrens Naadegerninger evindelig, jeg vil kundgøre din Sandhed med min Mund fra Slægt til Slægt.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Thi jeg har sagt: Din Naade skal bygges op evindelig, i Himlene skal du grundfæste din Sandhed:
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 „Jeg har gjort en Pagt med min udvalgte, jeg har tilsvoret David, min Tjener:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 Evindelig vil jeg stadfæste din Sæd, og jeg har bygget din Trone fra Slægt til Slægt.” (Sela)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Og Himlene, Herre! skulle prise din underfulde Gerning og din Sandhed i de helliges Menighed.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Thi hvem i Skyen kan maale sig med Herren? hvo er Herren lig iblandt Gudernes Børn?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 en Gud saare frygtelig i de helliges hemmelige Raad og forfærdelig over alle, som ere trindt omkring ham!
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Herre, Gud Zebaoth! hvo er som du stormægtig, o Herre? og din Sandhed er trindt omkring dig.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Du hersker over det hovmodige Hav; naar dets Bølger rejse sig, da bringer du dem til at lægge sig.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Du knuste Rahab, saa den blev som den ihjelslagne, du bortspredte dine Fjender med din stærke Arm.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Dig tilhøre Himlene, dig tilhører ogsaa Jorden, du har grundfæstet Jorderige og, hvad deri er.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Du skabte Norden og Sønden, Thabor og Hermon fryde sig i dit Navn.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Du har en Arm med Styrke, din Haand er stærk, din højre Haand er ophøjet.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Retfærdighed og Dom ere din Trones Befæstning, Miskundhed og Sandhed gaa frem for dit Ansigt.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Saligt er det Folk, som kender Frydesangen; Herre! i dit Ansigts Lys vandre de.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 I dit Navn skulle de fryde sig den ganske Dag, og i din Retfærdighed ophøjes de.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Thi du er deres Styrkes Pris, og i din Velbehagelighed ophøjer du vort Horn.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Thi Herren er vort Skjold og den Hellige i Israel vor Konge.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Da talte du til din Hellige i et Syn og sagde: Jeg har beredet Hjælp ved en Kæmpe, jeg har ophøjet en udvalgt ud af Folket.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 Jeg har fundet David, min Tjener, jeg har salvet ham med min hellige Olie.
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Ved ham skal min Haand holde fast, og min Arm skal styrke ham.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 Fjenden skal ikke plage ham, og en uretfærdig Mand skal ikke trænge ham.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Men jeg vil sønderknuse hans Modstandere for hans Ansigt og slaa dem, som hade ham.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Men min Sandhed og min Miskundhed skulle være med ham, i mit Navn skal hans Horn ophøjes.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Og jeg vil udstrække hans Haand til Havet og hans højre Haand til Floderne.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Han skal paakalde mig og sige: Du er min Fader, min Gud og min Frelses Klippe.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Og jeg vil gøre ham til den førstefødte, til den højeste over Kongerne paa Jorden.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Jeg vil bevare ham min Miskundhed evindelig, og min Pagt skal holdes ham trolig.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Og jeg vil lade hans Sæd bestaa evindelig, og hans Trone, saa længe Himmelens Dage vare.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Dersom hans Børn forlade min Lov, og de ikke vandre i mine Befalinger,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 dersom de vanhellige mine Skikke og ikke holde mine Bud:
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Da vil jeg hjemsøge deres Overtrædelse med Riset og deres Misgerning med Plager.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Men min Miskundhed vil jeg ikke tage fra ham og ikke svige min Sandhed.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Jeg vil ikke vanhellige min Pagt og ikke forandre det, som er gaaet over mine Læber.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Eet har jeg svoret ved min Hellighed, jeg vil ikke lyve for David:
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Hans Sæd skal blive evindelig, og hans Trone som Solen for mig;
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 den skal befæstes som Maanen evindelig; og Vidnet i Skyen er trofast. (Sela)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Men nu har du forkastet og foragtet ham, du er fortørnet paa din Salvede.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Du har tilintetgjort Pagten med din Tjener, du har vanhelliget hans Krone ned i Støvet.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Du har nedrevet alle hans Mure, du har bragt Ødelæggelse over hans Befæstninger.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Alle, som gik forbi paa Vejen, have plyndret ham, han er bleven til Spot for sine Naboer.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Du har ophøjet hans Modstanderes højre Haand, du har glædet alle hans Fjender.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Ja, du lader hans skarpe Sværd vige tilbage og har ikke ladet ham bestaa i Krigen.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Du har ladet hans Glans høre op og kastet hans Trone til Jorden.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Du har forkastet hans Ungdoms Dage, du har skjult ham med Haan. (Sela)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Hvor længe, Herre! vil du skjule dig evindelig? hvor længe skal din Harme brænde som Ild?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Kom i Hu, hvad en Levetid er, til hvilken Forfængelighed du har skabt alle Menneskens Børn?
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Hvo er den Mand, som lever og ikke skal se Døden? som kan fri sin Sjæl fra Dødsrigets Vold? (Sela) (Sheol )
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
49 Herre! hvor ere dine forrige Naadegerninger, som du tilsvor David i din Sandhed?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Herre! kom dine Tjeneres Forsmædelse i Hu, som jeg bærer i min Barm, den fra alle de mange Folkefærd,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 med hvilken dine Fjender have bespottet, Herre! med hvilken de have bespottet din Salvedes Fodspor.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Lovet være Herren evindelig! Amen, ja, amen.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!