< Salme 78 >
1 Mit Folk! vend dine Øren til min Lære, bøjer eders Øren til min Munds Tale!
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Jeg vil oplade min Mund med Ordsprog, jeg vil udgyde mørke Taler fra fordums Tid,
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 dem, som vi have hørt og vide, og vore Fædre have fortalt os.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Dette ville vi ikke dølge for deres Børn, for den Slægt, som kommer herefter, men forkynde Herrens megen Pris og hans Styrke og hans underfulde Gerninger, som han har gjort.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Han oprettede et Vidnesbyrd i Jakob og satte en Lov i Israel, i hvilken han bød vore Fædre at kundgøre dem for deres Børn,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 paa det den Slægt, som kom herefter, de Børn, som skulde fødes, kunde vide det, at de kunde staa op og fortælle det for deres Børn,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 og at de maatte sætte deres Haab paa Gud og ikke glemme Guds Gerninger, men bevare hans Bud;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 og at de ikke skulde vorde som deres Fædre, en modvillig og genstridig Slægt, en Slægt, som ikke beredte sit Hjerte, og hvis Aand ikke holdt trofast ved Gud.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Efraims Børn vare rustede Bueskytter, men svigtede paa Stridens Dag.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 De holdt ikke Guds Pagt og vægrede sig ved at vandre i hans Lov.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Og de glemte hans Gerninger og hans underfulde Ting, som han havde ladet dem se.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 For deres Fædre havde han gjort Undere i Ægyptens Land, paa Zoans Mark.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Han adskilte Havet og lod dem gaa igennem og optaarnede Vandet som en Dynge.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Og han ledede dem om Dagen ved Skyen og den ganske Nat ved Ildens Lys.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Han kløvede Klipper i Ørken og gav dem at drikke som af store Dyb.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Og han lod Bække strømme frem af Klippen og lod Vand rinde ned som Floder.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Men de bleve endnu ved med at synde imod ham, med at være genstridige imod den Højeste i Ørken.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Og de fristede Gud i deres Hjerte, saa at de begærede Mad for deres Lyst.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Og de talte imod Gud; de sagde: Mon Gud kan berede et Bord i Ørken?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Se, han har slaget Klippen, saa at der flød Vand, og Bækkene løb over; mon han og kan give Brød; mon han kan skaffe Kød for sit Folk?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Derfor, da Herren hørte det, blev han fortørnet; og en Ild optændtes imod Jakob, og en Vrede opkom imod Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 fordi de ikke troede paa Gud og ikke forlode sig paa hans Frelse.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Og han bød Skyerne heroventil og oplod Himlenes Døre.
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Og han lod Man regne paa dem til at æde og gav dem Himmelkorn.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Hver aad de stærkes Brød; han sendte dem Mad til Mættelse.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Han lod Østenvejr fare frem under Himmelen og førte Søndenvejr frem ved sin Styrke.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Og han lod Kød regne ned over dem som Støv og flyvende Fugle som Havets Sand.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Og han lod dem falde midt i sin Lejr, trindt omkring sine Boliger.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Og de aade og bleve saare mætte; han tilførte dem det, som de havde faaet Lyst til.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 De havde ikke styret deres Lyst, deres Mad var endnu i deres Mund:
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Da opsteg Guds Vrede imod dem, og han ihjelslog nogle iblandt de kraftigste af dem; og han nedslog de unge Mænd i Israel.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Med alt det syndede de endnu og troede ikke paa hans underfulde Gerninger.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Derfor lod han deres Dage svinde hen i Forfængelighed og deres Aar i Forskrækkelse.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Naar han slog dem ihjel, da søgte de ham, og de vendte om og søgte Gud aarle.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Og de kom i Hu, at Gud var deres Klippe, og Gud, den Højeste, deres Genløser.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Men de talte slesk for ham med deres Mund og løj for ham med deres Tunger.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Men deres Hjerte var ikke fast med ham, og de bleve ikke bestandige i hans Pagt.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Dog, han er barmhjertig, han soner Misgerning og fordærver ikke; han vendte sin Vrede mangfoldige Gange bort fra dem og lod ej sin Harme helt bryde frem.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Og han kom i Hu, at de vare Kød, et Aandepust, som farer hen og ej kommer tilbage.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Hvor tit vare de genstridige imod ham i Ørken, bedrøvede ham i de øde Steder.
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Og de fristede Gud paany og mestrede den Hellige i Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 De kom ikke hans Haand i Hu paa den Dag, da han udløste dem af Nød;
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 da han satte sine Tegn i Ægypten og sine Undere paa Zoans Mark;
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 da han forandrede deres Floder til Blod og deres Strømme, saa at de ikke kunde drikke af dem;
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 og han sendte alle Haande Utøj paa dem, som aad dem, og Frøer, som voldte dem Fordærvelse;
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 og han gav Kornormen deres Grøde og Græshoppen deres Arbejde;
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 han slog deres Vintræer med Hagelen og deres Morbærtræer med Isstykker;
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 og han overantvordede deres Dyr til Hagelen og deres Kvæg til Lynene;
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 han sendte sin grumme Vrede paa dem, Harme og Fortørnelse og Angest, en Sending af Ulykkesbud;
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 han banede Vej for sin Vrede, han sparede ikke deres Sjæl fra Døden, og han overantvordede deres Liv til Pesten;
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 og han slog alle førstefødte i Ægypten, Kraftens Førstegrøde i Kams Telte;
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 men sit Folk lod han drage ud som Faareflokken og førte dem i Ørken som Hjorden;
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 og han ledede dem tryggelig, at de ikke flygtede; men Havet skjulte deres Fjender.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Og han førte dem til sin Helligheds Landemærke, til dette Bjerg, som hans højre Haand havde forhvervet;
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 og han uddrev Hedningerne for deres Ansigt og lod disses Land tilfalde dem som Arvedel; og han lod Israels Stammer bo i deres Telte.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Men de fristede Gud, den Højeste, og vare genstridige imod ham og agtede ikke paa hans Vidnesbyrd.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Og de vendte sig bort og bleve troløse som deres Fædre, de sloge tilbage som en falsk Bue.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Og de opirrede ham ved deres Høje og gjorde ham nidkær ved deres udskaarne Billeder.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Der Gud det hørte, da blev han fortørnet, og han foragtede Israel saare.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Han forlod Boligen i Silo, det Paulun, som han havde sat til at bo udi iblandt Menneskene.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Og han gav sin Magt i Fangenskab og sin Herlighed i Fjendens Haand.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Og han overantvordede sit Folk til Sværd og fortørnedes paa sin Arv.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Ild fortærede deres unge Mandskab, og deres Jomfruer fik ingen Brudesang.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Deres Præster faldt for Sværdet, og deres Enker begræd dem ikke.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Da opvaagnede Herren som en sovende, som en Helt, der jubler af Vin.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Og han slog sine Fjender tilbage, han gjorde dem en evig Skam.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Og han forkastede Josefs Telt og udvalgte ikke Efraims Stamme;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 men han udvalgte Judas Stamme, Zions Bjerg, som han elskede.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Og han byggede sin Helligdom lig Højderne, lig Jorden, hvilke han har grundfæstet evindelig.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Og han udvalgte David, sin Tjener, og tog ham fra Faarestierne;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 fra Faarene, som gave Die, lod han ham komme at vogte Jakob sit Folk og Israel sin Arv.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Og han vogtede dem efter sit Hjertes Oprigtighed og ledede dem med forstandig Haand.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.