< Salme 74 >
1 Gud! hvorfor har du forkastet os evindelig; din Vrede ryger imod din Græsgangs Hjord.
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Kom din Menighed i Hu, som du forhvervede i fordums Tid, som du genløste, til at være din Arvs Stamme, dette Zions Bjerg, som du bor paa.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Opløft dine Trin til de evigt ødelagte Steder; Fjenden har handlet ilde med alting i Helligdommen.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Dine Modstandere have brølet midt i din Forsamling, de have sat deres Tegn op til Tegn.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 Det ser ud, som naar een hæver Økserne højt imod Træets tætte Grene.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 Og nu de Ting, som vare derudi af udskaaret Arbejde, dem have de sønderslaaet med Økser og Hamre.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 De have sat Ild paa din Helligdom, de have vanhelliget dit Navns Bolig, lige til Jorden.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 De have sagt i deres Hjerte: Lader os kue dem tilsammen; de have opbrændt alle Guds Forsamlingshuse i Landet.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 Vi se ikke vore egne Tegn; der er ingen Profet ydermere og ingen hos os, som ved, hvor længe det skal vare.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 Gud! hvor længe skal Modstanderen forhaane, skal Fjenden foragte dit Navn evindelig?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Hvorfor drager du din Haand, din højre Haand tilbage? Tag den ud fra din Barm, ødelæg dem!
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Gud er dog min Konge fra fordums Tid, som skaber Frelse midt paa Jorden.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Du adskilte Havet med din Styrke, du sønderbrød Havuhyrernes Hoveder i Vandene.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 Du knuste Leviathans Hoveder, du gav Folket i Ørken den til Spise.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Du lod Kilde og Bæk bryde frem, du udtørrede de altid rindende Floder.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 Dagen hører dig til, Natten hører dig ogsaa til, du har beredt Lys og Sol.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 Du har sat alle Jordens Grænser; Sommer og Vinter, dem har du beskikket.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Kom dette i Hu: Fjenden forhaanede Herren, og et Folk af Daarer foragtede dit Navn.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 Giv ikke vilde Dyr din Turteldues Sjæl, glem ikke dine elendiges Liv evindelig!
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Se til Pagten; thi Jordens mørke Steder ere fulde af Volds Boliger.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 Lad den ringe ikke vende beskæmmet tilbage, lad den elendige og fattige love dit Navn!
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Gud! gør dig rede, udfør din Sag; kom din Forhaanelse i Hu, som dig sker af Daaren den ganske Dag.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Glem ikke dine Fjenders Røst, dine Modstanderes Bulder, som stiger altid op.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.