< Salme 72 >
1 Gud! giv Kongen dine Domme og Kongens Søn din Retfærdighed,
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 at han kan dømme dit Folk med Retfærdighed og dine elendige med Retvished.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Lad Bjergene bære Fred for Folket og Højene ligesaa ved Retfærdigheden.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Han skal skaffe de elendige iblandt Folket Ret, han skal frelse den fattiges Børn og knuse Voldsmanden.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 De skulle frygte dig, saa længe Solen er til, og saa længe Maanen lyser, fra Slægt til Slægter.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Han stige ned som Regn paa den slaaede Eng, som Draaber, der væde Jorden!
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 I hans Dage blomstre den retfærdige og megen Fred, indtil Maanen ikke er mere!
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Og han regerer fra Hav til Hav, og fra Floden indtil Jordens Ende!
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 De, som bo i Ørken, skulle bøje sig for hans Ansigt, og hans Fjender skulle slikke Støv.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Konger fra Tarsis og Øerne skulle bringe Skænk! Konger fra Skeba og Seba skulle fremføre Gave.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Og alle Konger skulle tilbede for ham; alle Hedninger skulle tjene ham.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Thi han skal fri den fattige, som raaber, samt den elendige, som ingen Hjælper har.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Han skal spare den ringe og fattige og frelse de fattiges Sjæle.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Han skal udløse deres Sjæl fra Undertrykkelse og fra Vold, og deres Blod skal være dyrebart for hans Øjne.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Og de skulle leve og give ham af Skebas Guld og altid bede for ham, love ham den ganske Dag.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Der vorde Overflod af Korn i Landet paa Bjergenes Top; dets Frugt suse som Libanon, og Folk blomstre frem af Staden som Urter paa Jorden!
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Hans Navn blive evindelig; saa længe Solen lyser, forplante sig hans Navn, og de skulle velsigne sig selv i ham, alle Hedninger skulle prise ham salig!
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Lovet være den Herre Gud, Israels Gud, han, som ene gør underfulde Ting!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Og lovet være hans Æres Navn evindelig; og al Jorden fyldes med hans Ære! Amen, ja, Amen!
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Davids, Isajs Søns Bønner have Ende.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.