< Salme 71 >

1 Herre! jeg forlader mig paa dig, lad mig ikke beskæmmes evindelig!
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Red mig ved din Retfærdighed og udfri mig; bøj dit Øre til mig og frels mig!
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Vær mig en Klippe til Bolig, hvorhen jeg altid kan ty, du, som har befalet at frelse mig; thi du er min Klippe og min Befæstning.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Min Gud! udfri mig af en ugudeligs Haand, af dens Haand, som gør Uret, og som undertrykker.
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 Thi du er min Fortrøstning; Herre, Herre! du er min Tillid fra min Ungdom af.
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 Paa dig har jeg forladt mig fast fra Moders Liv, du har draget mig af min Moders Skød; min Lovsang er altid om dig.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 Jeg har været for mange som et Under; men du er min stærke Tillid.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 Lad min Mund fyldes med din Lovsang, den ganske Dag med din Pris.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Forkast mig ikke i Alderdommens Tid; forlad mig ikke, naar min Kraft forgaar!
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 Thi mine Fjender tale imod mig, og de, som tage Vare paa min Sjæl, raadføre sig med hverandre,
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 sigende: Gud har forladt ham, forfølger og griber ham; thi der er ingen, som frier.
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 Gud! vær ikke langt fra mig; min Gud! skynd dig at hjælpe mig!
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Lad dem beskæmmes, fortæres, som staa imod min Sjæl, lad dem iføres Forhaanelse og Skændsel, som søge min Ulykke.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 Men jeg vil altid haabe, og al din Pris vil jeg endnu mangfoldiggøre.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 Min Mund skal fortælle din Retfærdighed, din Frelse den ganske Dag; thi jeg ved ikke Tal derpaa.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 Jeg vil komme frem med Herrens, Herrens vældige Gerninger; jeg vil minde om din Retfærdighed, din alene.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 Gud! du har lært mig fra min Ungdom af, og indtil nu kundgør jeg dine underfulde Gerninger.
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Ja, endog indtil Alderdommen og de graa Haar, o Gud! forlad mig ikke; indtil jeg kan kundgøre din Arm for Efterslægten, din Kraft for hver den, som komme skal.
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 Og din Retfærdighed strækker sig, o Gud! til det høje; du, som har gjort store Ting, Gud! hvo er som du?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 Du, som har ladet mig se mange Angester og Ulykker, du vil gøre mig levende igen og hente mig op igen fra Jordens Afgrunde.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Gør min Herlighed stor og trøst mig igen!
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 Og jeg vil takke dig med Strengeleg for din Sandhed, min Gud! jeg vil synge for dig til Harpe, du Hellige i Israel!
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 Mine Læber skulle juble, naar jeg synger for dig; ja, min Sjæl, som du har genløst.
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 Og min Tunge skal tale den ganske Dag om din Retfærdighed; thi de ere beskæmmede, thi de ere blevne til Skamme, som søge min Ulykke.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Salme 71 >