< Salme 37 >
1 Af David. Lad din Vrede ikke optændes imod de onde; vær ikke nidkær imod dem, som gøre Uret;
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 thi de skulle hastelig falme som Græs, og visne som grønne Urter.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Forlad dig paa Herren og gør godt; bo i Landet og nær dig trolig;
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 og forlyst dig i Herren, saa skal han give dig dit Hjertes Begæring.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Vælt din Vej paa Herren og forlad dig paa ham, han skal gøre det.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 Og han skal føre din Retfærdighed frem som Lyset og din Ret som Middagsglansen.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Ti for Herren og forvent ham; lad din Vrede ikke optændes imod den Mand, hvis Vej lykkes, imod den Mand, som øver Underfundighed.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Lad af fra Vrede og lad Heftighed fare, lad din Vrede ikke optændes, den er kun til at gøre ondt.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 Thi de onde skulle udryddes, men de, som bie efter Herren, de skulle arve Landet.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Og endnu et lidet, saa er den ugudelige ikke mere; og naar du giver Agt paa hans Sted, da er han borte.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 Men de sagtmodige skulle arve Landet og forlyste sig over stor Fred.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 Den ugudelige optænker Skalkhed imod den retfærdige og skærer Tænder imod ham.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 Herren skal le ad ham; thi han ser, at hans Dag er kommen.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 De ugudelige have uddraget Sværd og spændt deres Bue at fælde en elendig og fattig, at tage Livet af dem, som vandre i Oprigtighed.
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Deres Sværd skal komme i deres eget Hjerte, og deres Buer skulle sønderbrydes.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Det lidet, som den retfærdige har, er bedre end mange ugudeliges Gods.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 Thi de ugudeliges Arme skulle sønderbrydes; men Herren opholder de retfærdige.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 Herren kender de retsindiges Dage, og deres Arv skal blive evindelig.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 De skulle ikke beskæmmes i den onde Tid, og de skulle mættes i Hungers Dage.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 Thi de ugudelige skulle omkomme, ja, Herrens Fjender, som Engenes Pragt; de ere forsvundne, i Røg forsvundne.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 En ugudelig maa tage til Laans, og kan ikke betale; men en retfærdig kan forbarme sig og giver.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 Thi Herrens velsignede skulle arve Landet; men hans forbandede skulle udryddes.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 Af Herren stadfæstes en Mands Gang, og han vil have Velbehag til hans Vej.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Naar han falder, bliver han ikke liggende; thi Herren holder fast ved hans Haand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Jeg har været ung og er bleven gammel; men jeg har ikke set en retfærdig forladt eller hans Sæd at søge efter Brødet.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 Han forbarmer sig den ganske Dag og laaner ud, og hans Sæd skal blive til en Velsignelse.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Vig fra ondt, og gør godt, saa skal du blive boende evindelig.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 Thi Herren elsker Ret og forlader ikke sine hellige, de ere bevarede evindelig; men de ugudeliges Sæd er udryddet.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 De retfærdige skulle arve Landet og bo der evindelig.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 En retfærdigs Mund skal tale Visdom, og hans Tunge skal forkynde Ret.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 Hans Guds Lov er i hans Hjerte; hans Trin skulle ikke glide.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 En ugudelig lurer paa den retfærdige og søger efter at dræbe ham.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Herren skal ikke overlade ham i hans Haand og ej kende ham skyldig, naar han dømmes.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Bi efter Herren og var paa hans Vej, saa skal han ophøje dig til at arve Landet; du skal se paa de ugudeliges Udryddelse.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 Jeg saa en ugudelig, en Voldsmand; han udbredte sig som et grønt Rodskud.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Men han forsvandt og se, han var ikke mere; og jeg søgte efter ham, men han fandtes ikke.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Tag Vare paa den retsindige, og se hen til den oprigtige, thi Fredens Mand har en Fremtid.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 Men Overtrædere skulle ødelægges til Hobe; de ugudeliges Fremtid er borte.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 Men de retfærdiges Frelse er af Herren, han er deres Styrke i Nødens Tid.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 Og Herren skal hjælpe dem og udfri dem; han skal udfri dem fra de ugudelige og frelse dem; thi de have forladt sig paa ham.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.