< Salme 35 >
1 Af David. Herre! træt med dem, som trætte med mig; strid imod dem, som stride imod mig.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Grib Skjold og Værge, og staa op at hjælpe mig.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Tag Spydet frem og afskær Vejen for mine Forfølgere; sig til min Sjæl: Jeg er din Frelse.
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Lad dem, som søge efter mit Liv, blues og blive til Skamme; lad dem, som ville mig ondt, vige tilbage og blive beskæmmede.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Lad dem blive som Avner for Vejret, og Herrens Engel støde dem bort.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Lad deres Vej blive mørk og slibrig, og Herrens Engel forfølge dem.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 Thi de skjulte uden Skel deres Garn imod mig i en Grube, de grove en Grav for min Sjæl uden Skel.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Lad Ødelæggelse komme over dem, uden at de vente det; og lad deres Garn, som de skjulte, fange dem, lad dem falde deri til Ødelæggelse.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Men min Sjæl skal glæde sig i Herren, den skal fryde sig i hans Frelse.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 Alle mine Ben skulle sige: Herre! hvo er som du? du, som frier en elendig fra den, som er ham for stærk, ja, en elendig og fattig fra den, som udplyndrer ham.
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Der staa træske Vidner op, de affordre mig det, som jeg ikke ved.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 De betale mig ondt for godt, min Sjæl føler sig forladt.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Men der de vare syge, iførte jeg mig Sæk, jeg plagede min Sjæl med Faste, og jeg bad med Hovedet sænket mod min Barm.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Jeg omgikkes med ham, som han havde været min Ven og Broder; jeg gik i Sørgeklæder og var nedbøjet som en, der sørger for sin Moder.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 Men da jeg kom til at halte, glædede de sig og flokkedes; Uslinger flokkedes om mig, og jeg vidste af intet; de sønderslede og tav ikke.
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Iblandt vanhellige og frække Spottere skare de Tænder imod mig.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Herre! hvor længe vil du se til? udfri min Sjæl fra deres Ødelæggelse, min eneste fra de unge Løver.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 Jeg vil takke dig i en stor Forsamling, jeg vil love dig iblandt et talrigt Folk.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Lad dem, som ere mine Fjender uden Skel, ikke glædes over mig, eller dem, som hade mig uforskyldt, give Vink med Øjnene.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 Thi de tale ikke Fred; men imod de stille i Landet optænke de svigefulde Anslag.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Og de lode deres Mund vidt op imod mig; de sagde: Ha, ha! vort Øje har set det.
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Herre! du har set det; ti ikke, Herre! vær ikke langt fra mig.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Vaagn op og vær vaagen for min Ret, for min Sag, min Gud og min Herre!
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Herre, min Gud! døm mig efter din Retfærdighed, og lad dem ikke glæde sig over mig,
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 at de ikke skulle sige i deres Hjerte: „Ha, ha! det var vor Lyst!” Lad dem ikke sige: „Vi have opslugt ham!”
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Lad dem, som glæde sig ved min Ulykke, til Hobe blues og blive til Skamme; lad dem, som gøre sig store imod mig, klædes med Skam og Skændsel.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Lad dem frydes og glædes, som have Lyst til min Retfærdighed, og lad dem altid sige: Herren bør storlig loves, han, som har Lyst til sin Tjeners Fred.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 Saa skal min Tunge tale om din Retfærdighed, om din Pris den ganske Dag.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.