< Salme 33 >
1 Synger med Fryd, I retfærdige, i Herren! Lovsang sømmer sig for de oprigtige.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Takker Herren med Harpe; og leger for ham paa Psaltre med ti Strenge.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Synger ham en ny Sang, leger lifligt paa Strengeleg med Frydeklang.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 Thi Herrens Ord er ret, og al hans Gerning er trofast.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Han elsker Retfærdighed og Dom; Jorden er fuld af Herrens Miskundhed.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Himlene ere gjorte ved Herrens Ord og al deres Hær ved hans Munds Aande.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Han holder Vandet sammen i Havet som en Dynge; han lægger de dybe Vande i Forraadskamre.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Al Jorden frygte Herren! alle Verdens Indbyggere bæve for ham!
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 Thi han talte, og det skete; han bød, saa stod det der.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 Herren gjorde Hedningernes Raad til intet, han forstyrrede Folkenes Tanker.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 Herrens Raad bestaar evindelig, hans Hjertes Tanker fra Slægt til Slægt.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Saligt er det Folk, hvis Gud Herren er, det Folk, som han udvalgte sig til Arv.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 Herren skuede ud fra Himmelen, han saa alle Menneskens Børn.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Han saa ned fra sit Højsæde til alle Jordens Indbyggere.
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 Han er den, som danner deres Hjerter til Hobe, som agter paa alle deres Gerninger.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 En Konge frelses ikke ved stor Magt, en vældig fries ikke ved stor Kraft.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Hesten slaar fejl til Frelse og kan ikke redde ved sin store Styrke.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Se, Herrens Øje er til dem, som ham frygte, som haabe paa hans Miskundhed,
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 for at fri deres Sjæl fra Død og holde dem i Live i Hungersnøden.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Vor Sjæl bier efter Herren, han er vor Hjælp og vort Skjold.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 Thi i ham glædes vort Hjerte; thi vi forlade os paa hans hellige Navn.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Herre! din Miskundhed være over os, ligesom vi haabe paa dig!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.